ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masarautar Mubi Da Kyakkyawan Shugabancin Sarki Alhaji Abubakar Isa Ahmadu

by Muh'd Shafi'u Saleh
3 years ago
Mubi

Masarautar Mubi da ke arewa maso gabashin Nijeriya, wacce ke da nisan kimanin kilomita 220 daga Yola fadar Jihar Adamawa, baya ga kasancewar masarauta ita ce masarauta ta biyu mafi girma da shahara a jihar, masarautar ta kuma shahara ta fannonin noma, kiwo da kasuwanci. 

Mazauna masarautar wacce al’ummar Fulani suka kirkira a karni na 18, ta kasance karkashin Daulan Mandarawa, na lokaci mai tsawo kafin zuwa Jihadin Shehu Usmanu Ibn Fodiyo da ta koma karkashin Daular Musulunci da Modibbo Adama ya jagoranta a yankin.

  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne
  • Tinubu Ga Peter Obi: Ka Gargaɗi Magoya Bayanka Kan Ɓata Min Suna

A shekara ta 1820 ne, jama’ar Mubi da kiwayen masarautar suka mika wuya ga Jihadin Shehu Usmanu bisa jagorancin Modibbo Adama, wanda daga baya ake kira da ‘Masarautar Fombina Adamawa.

ADVERTISEMENT

A shekarar 1890, masarautar Mubi ta nemi ta balle daga masarautar Fombina lokacin da Marigayi Lamido Zubairu ke kan garagar mulkin masarautar Fombina a matsayin sarki.

Da karfin tsiya, Turawan Jamus suka amshi iko da masarautar a shekarar 1903, suka kuma rike masarautar a matsayar ita ce cibiyar gudanar da mulkin Jamus-Kamaru har lokacin da Turawan Birtaniya suka kwace iko da masarautar a shekarar 1914.

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

Masarautar Mubi da kiwaye ta kasance karkashin Birtaniya-Kamaru bisa hadin gwiwar kasashen Turawa har a shekarar 1922.

A shekarar 1961, masarautar Mubi ta kasance cikakkiyar bangare daga cikin bangarorin kasar Nijeriya.

A tsawon wadannan shekaru, masarautar Mubi na amsar umurni daga masarautar Fombina, domin kuwa masarautar Lamido Adamawa (Fombina), ke nada hakimi a masarautar ta Mubi a lokacin tsohon tsarin gudanarwar mulkin Nijeriya, kafin da bayan kirkiro da sabbin jihohi ciki har da jihohi daga tsohowar Jihar Gongola a shekarar 1976.

Daga lokacin ne kuma, Gwamna Abubakar Sale Michika, a shekarar 1989, ya mayar da masarautar ta koma mai cin gashin kanta, ta yadda sarkin masarautar ya zama mai martaba na daya mai makon hakimi.

A lokacin guda kuma aka nada mai Martaba Isa Ahmadu a matsayin sarki mai daraja ta daya na masarautar Mubi, da ta hada kananan hukumomin Maiha, Hong, Michika, Madagali, inda masarautar ke nada musu hakimai a yau.

A shekarar 1991, aka nada Alhaji Abubakar Isa Ahmadu a matsayin Mai Martaba Sarkin Mubi, bayan rasuwar Mahaifinsa, to sai dai duk da samun cin gashin kai da masarautar ta samu daga masarautar Fombina, masarautar Mubi na da kyakkyawan alaka da dangantaka ta kut-da-kut da masarautar Fombina a tsawon wadannan shekarun.

Wani muhimmin abu game da masarautar Mubi shi ne, rikici ko tashin-tashinan da ake samu tsakanin manoma da makiyaya ko tsakanin kabilu a wasu yankunan Jihar Adamawa ba a taba samun irinsa a masarautar Mubi ba. Garin Mubi bai taba fuskantar wata barazanar da ta wuce ta Boko Haram a shekarar 2014 ba.

Zaman lafiya da kwanciyar hankali hadi da fahimtar junan da masarautar ta samar a tsakankanin jama’a da kabilu mabambanta ya haifar mata ci gaban da zama cibiyar kasuwancin jihar, kuma ta ci gaba da zama babbar kasuwar Shanu ba kawai a arewa maso gabas ko Nijeriya ba, kasuwar Shanu ta Mubi ta kasuwace ta kasa da kasa.

A masarautar Mubi ta yau da ta hada kananan hukumomi biyar, ba a taba samun wani manomin da ya yi noma kan burtalin shanu ba, saboda haka makiyaya ba su taba shiga gonar wani manomi ba, kasantuwar suna da hanyoyin da za su wuce da shanunsu su tafi kiwo ko kaura daga wuri zuwa wani wuri, kamar yadda makiyaya suka saba yi.

To sai dai, akwai masu ganin lokaci ya yi da za a samu karin kirkiro wata masarauta mai daraja ta daya daga yankin, lamarin da masu tunanin ke ganin zai taimaka ga samun saukin gudanarwa ga gwamnatin jiha dama ita kanta masarauta.

Da yake magana game da masarautar Mubi, Hassan Muhammad Oscer, ya ce “Babu abin da za mu ce game da mai martaba sai godiyar Allah, shekaru 31, yake a matsayin Sarkin Mubi ba mu taba samun rikici ya faru a tsakaninmu kabilusa na Fulani a yankin masarautarsa ba.

“Mutum ne wanda yake kokarin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin ko rikici tsakanin makiyaya da manoma ba a taba samu ba tun da aka kirkiri masarautar Mubi, haka kuma ba a taba samun damuwa tsakanin Fulani da sauran kabilu ba.

“Tun lokacin da ake tura hakimai daga masarautar Lamido, ba a samun matsala a yankin, daga lokacin da masarautar ta samu babban sarki mai daraja, sarkin ya maida hankali wajan hade kan al’umman yankin, muna zaune lafiya da fahimtar juna,” in ji Hassan Oscer.

Da yake magana kan batun raba masarautar kuwa Oscer cewa ya yi “Ba mu da wata matsala da sarkinmu, amma idan gwamnati ta ce tana da niyyar za ta yi abinta, babu mutumin da ya isa ya hana gwamnati, domin mu kanmu da sarakunan gargajiya malumanmu da fastocinmu ita ta ajiyemu muna karkashinta ne.

“Saboda haka idan gwamnati ta ce za ta yi ya rage mata da ‘yan majalisar dokoki, ba mu da muke karkashin Sarkin Mubi ko karkashin sarakunan gargajiya ba,” in ji Hassan Oscer.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
Labarai

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Manyan Labarai

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
Next Post
Obasanjo Ya Roki Marayun Borno Su Yafe Wa ‘Yan Ta’addar Da Suka Kashe Iyayensu

Obasanjo Ya Roki Marayun Borno Su Yafe Wa 'Yan Ta'addar Da Suka Kashe Iyayensu

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025
Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.