• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Cutar Sikari Na Fuskantar Karin Kudin Magani Da Kashi 200

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Masu Cutar Sikari Na Fuskantar Karin Kudin Magani Da Kashi 200
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan Nijeriya wadanda suke fama da cutar Sikari sun yi kira da gwamnatin tarayya da cewar ta cire harajin da ake biya na magunguna,da sauran kayan gwaji na cutar Sikari saboda yadda farashin magungunan ya karu ya kara sa wadanda suke fama da  cutar cikin mawuyacin hali na rayuwa.

Binciken da jaridar LEADERSHIP ta gudanar ya nuna mai fama da cutar Sikari a Nijeriya yana kashe Naira dubu talatin (#30,000) kowanne wata a wannan shekara ta muke ciki ta 2022, wannan kudin magani ne da kuma gwaji,wanda idan aka tuna a baya shekarar 2019 kudin Naira dubu goma ne (#10,000) ake biya.

Kwanturola-Janar Na NIS Ya Amince Da Nadin Tony Akuneme A Matsayin Sabon Kakakin Hukumar Na Kasa

Sauya Fasalin Naira Zai Karya Darajar Dalar Amurka Zuwa Naira 200 Duk Daya – EFCC

Duk wannan ma baa bin damuwa bane matsaslar ita ce shi maganin insulin da kwararru na cutar Sikari (endocrinologist), ba samun shi ake cikin sauki ba,yayiin da su kwararrun basu da yawa.Irin hakan ke kara sa masu fama da cutar shiga wani halin kaka- nika yi.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Wata kididdigar da ba a dade da samu ba ta nuna akwai ‘yan Nijeriya milyan shida wadanda suke fama da cutar,wannan ma kamar dai shi hasashen na kwararru alkalumman sun zarce haka.Saboda kashi biyu bisa uku na masub fama da cuta a Nijeriya ba a ma gane ko su wanene ba,wannan ya kara yawan masu cutar da wahalar da suke shada kuma mace- mace sanadiyar cutar.

Duk da shan wahalar da masu fama da cutar ke yi,kwararru kan al’amarin daya shafi cutar Sikari basu da yawa a Nijeriya,domin kuwa an yi kididdigar cewar ga mutane 600,000 masu fama da cutar,kwararre daya take ne zai kula da su.

Babbar matsalar cutar a Nijeriya ita ce tana kara yaduwa yayin da maganinta yake da matsalar samu cikin sauki,idan aka yi la’akari da yadda farashin kayan gwaji da magani ke kara tashin gwauron zabo.Wannan ba a Nijeriya kadai ba har ma da sauran kasashe da suke cikin ‘yan rabbana ka wadata mu ko kuma, matsakaita wadanda kudaden da suke samu basu taka kara sun karya ba.

Duk da yake an wallafa wani rahoto kan yadda ake luar da masu fama da cutar,na wata gidauniyar yadda ake samun maganin, wanda  wata kungiya ce mai zaman kanta a kasar Netherland,ta bayyana cewa ana sa ran nan da shekara ta 2030 za a samutane milyan 570 da suke fama da cutar. Yayin da kuma zuwa shekarar 2045 adadin na iya kaiwa milyan 700,

Babban jami’in gidauniyar da za a samu maganin Dakta Jayasree Iyer, ya bayyana nan da shekara ta 2045 cutar zata kar4u da milyan takwas.

Ya ce shi al’amarin da yasa kudaden kulawa da cutar suka karu abin ya wuce zamantakewa akwai ma matsalar halin rayuwar da ke ciki,inda ya kara da cewa“Kudaden da ake kashewa domin kulawa da msu cutar Sikari a Nijeriya da sauran kasashen Afirka abin ya kaidalar Amurka bilyan 12.5,wannan al’amarin kuma ya nuna gaskiyar mutane na biyan kudade masu yawa wajen magani na insulin”.

Ya ce yawan kudaden da mai fama da cutar Sikari zai kashe dala dari biyar ($500)a ko wacce shekara,wannan ba karamin abu bane musamman ma ace idan shi mara lafiyar zai biya gaba daya ko kuma wani abu daga cikin aljihunsa.

Wani kwararren dan jarida a Nijeriya, Mista. Sam Eferaro, wanda aka gano ya kamu da cutar Sikari fiye da shera goma ya bayyanawa LEADERSHIP cewa yanzu yana kashe tsakanin Naira 25,000 ko Naira 30,000 kowanne wata saboda maganin cutar Sikari, ya kara da a shekarar 2019 yana kammmala dukan abubuwan maganin kasa da Naira 10,000.

Eferaro ya ce ita tsadar ko karin kudin bai tsaya kan maganin cutar Sikari kadai ba,inda ya kara da gaba daya fashin magungunan sun karu,  sai dai kuma mutane “masu fama da cutar Sikari sune suke ji a jikinsu saboda dole su cigaba da yin hakan matsawar suna son kada cutarta kara samun matsala.

“Haka take ga sauran wadanda suke fama da cututtuka kamar Hawan jini da sauran cututtuka wadanda basu saurin yaduwa.

Ya kara da cewa sauran kasashen Afirka kamar su Kamaru da Ghana suna da wasu tsare- tsare ga mutanen da suke fama da cutar Sikari,musamman ma yara.

“Babu irin wancan tsarin a Nijeriya domin gwamnatin Nijeriya bata da wani tsari ko wani kokarin da take yi na rage masu wadanda suke fama da cutar Sikari. Maimakon haka ma sai ga shi farashin magunguna da na’urar da ake bibiyar halin da mai cutar yake ciki, abin karuwa yake ko wacce shekara, saboda kudaden haraji da kuma na shigo da kaya daga kasashen waje, wadanda dole ne Kamfanonin hada magunguna suke biya domin shigo da magungunan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CutaMaganiSikariTsada
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Zama Misali A Fannin Inganta Ci Gaban Kasa Da Kasa

Next Post

Peng Liyuan Ta Ziyarci Dakin Adana Kayan Tarihi Na Fasaha Na Birnin Ayutthaya Na Thailand

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

8 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

13 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

19 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

23 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

24 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

2 days ago
Next Post
Peng Liyuan Ta Ziyarci Dakin Adana Kayan Tarihi Na Fasaha Na Birnin Ayutthaya Na Thailand

Peng Liyuan Ta Ziyarci Dakin Adana Kayan Tarihi Na Fasaha Na Birnin Ayutthaya Na Thailand

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.