ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Cutar Sikari Na Fuskantar Karin Kudin Magani Da Kashi 200

by Idris Aliyu Daudawa
4 years ago
Sikari

‘Yan Nijeriya wadanda suke fama da cutar Sikari sun yi kira da gwamnatin tarayya da cewar ta cire harajin da ake biya na magunguna,da sauran kayan gwaji na cutar Sikari saboda yadda farashin magungunan ya karu ya kara sa wadanda suke fama da  cutar cikin mawuyacin hali na rayuwa.

Binciken da jaridar LEADERSHIP ta gudanar ya nuna mai fama da cutar Sikari a Nijeriya yana kashe Naira dubu talatin (#30,000) kowanne wata a wannan shekara ta muke ciki ta 2022, wannan kudin magani ne da kuma gwaji,wanda idan aka tuna a baya shekarar 2019 kudin Naira dubu goma ne (#10,000) ake biya.

Kwanturola-Janar Na NIS Ya Amince Da Nadin Tony Akuneme A Matsayin Sabon Kakakin Hukumar Na Kasa

ADVERTISEMENT

Sauya Fasalin Naira Zai Karya Darajar Dalar Amurka Zuwa Naira 200 Duk Daya – EFCC

Duk wannan ma baa bin damuwa bane matsaslar ita ce shi maganin insulin da kwararru na cutar Sikari (endocrinologist), ba samun shi ake cikin sauki ba,yayiin da su kwararrun basu da yawa.Irin hakan ke kara sa masu fama da cutar shiga wani halin kaka- nika yi.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Wata kididdigar da ba a dade da samu ba ta nuna akwai ‘yan Nijeriya milyan shida wadanda suke fama da cutar,wannan ma kamar dai shi hasashen na kwararru alkalumman sun zarce haka.Saboda kashi biyu bisa uku na masub fama da cuta a Nijeriya ba a ma gane ko su wanene ba,wannan ya kara yawan masu cutar da wahalar da suke shada kuma mace- mace sanadiyar cutar.

Duk da shan wahalar da masu fama da cutar ke yi,kwararru kan al’amarin daya shafi cutar Sikari basu da yawa a Nijeriya,domin kuwa an yi kididdigar cewar ga mutane 600,000 masu fama da cutar,kwararre daya take ne zai kula da su.

Babbar matsalar cutar a Nijeriya ita ce tana kara yaduwa yayin da maganinta yake da matsalar samu cikin sauki,idan aka yi la’akari da yadda farashin kayan gwaji da magani ke kara tashin gwauron zabo.Wannan ba a Nijeriya kadai ba har ma da sauran kasashe da suke cikin ‘yan rabbana ka wadata mu ko kuma, matsakaita wadanda kudaden da suke samu basu taka kara sun karya ba.

Duk da yake an wallafa wani rahoto kan yadda ake luar da masu fama da cutar,na wata gidauniyar yadda ake samun maganin, wanda  wata kungiya ce mai zaman kanta a kasar Netherland,ta bayyana cewa ana sa ran nan da shekara ta 2030 za a samutane milyan 570 da suke fama da cutar. Yayin da kuma zuwa shekarar 2045 adadin na iya kaiwa milyan 700,

Babban jami’in gidauniyar da za a samu maganin Dakta Jayasree Iyer, ya bayyana nan da shekara ta 2045 cutar zata kar4u da milyan takwas.

Ya ce shi al’amarin da yasa kudaden kulawa da cutar suka karu abin ya wuce zamantakewa akwai ma matsalar halin rayuwar da ke ciki,inda ya kara da cewa“Kudaden da ake kashewa domin kulawa da msu cutar Sikari a Nijeriya da sauran kasashen Afirka abin ya kaidalar Amurka bilyan 12.5,wannan al’amarin kuma ya nuna gaskiyar mutane na biyan kudade masu yawa wajen magani na insulin”.

Ya ce yawan kudaden da mai fama da cutar Sikari zai kashe dala dari biyar ($500)a ko wacce shekara,wannan ba karamin abu bane musamman ma ace idan shi mara lafiyar zai biya gaba daya ko kuma wani abu daga cikin aljihunsa.

Wani kwararren dan jarida a Nijeriya, Mista. Sam Eferaro, wanda aka gano ya kamu da cutar Sikari fiye da shera goma ya bayyanawa LEADERSHIP cewa yanzu yana kashe tsakanin Naira 25,000 ko Naira 30,000 kowanne wata saboda maganin cutar Sikari, ya kara da a shekarar 2019 yana kammmala dukan abubuwan maganin kasa da Naira 10,000.

Eferaro ya ce ita tsadar ko karin kudin bai tsaya kan maganin cutar Sikari kadai ba,inda ya kara da gaba daya fashin magungunan sun karu,  sai dai kuma mutane “masu fama da cutar Sikari sune suke ji a jikinsu saboda dole su cigaba da yin hakan matsawar suna son kada cutarta kara samun matsala.

“Haka take ga sauran wadanda suke fama da cututtuka kamar Hawan jini da sauran cututtuka wadanda basu saurin yaduwa.

Ya kara da cewa sauran kasashen Afirka kamar su Kamaru da Ghana suna da wasu tsare- tsare ga mutanen da suke fama da cutar Sikari,musamman ma yara.

“Babu irin wancan tsarin a Nijeriya domin gwamnatin Nijeriya bata da wani tsari ko wani kokarin da take yi na rage masu wadanda suke fama da cutar Sikari. Maimakon haka ma sai ga shi farashin magunguna da na’urar da ake bibiyar halin da mai cutar yake ciki, abin karuwa yake ko wacce shekara, saboda kudaden haraji da kuma na shigo da kaya daga kasashen waje, wadanda dole ne Kamfanonin hada magunguna suke biya domin shigo da magungunan.

Sikari
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Peng Liyuan Ta Ziyarci Dakin Adana Kayan Tarihi Na Fasaha Na Birnin Ayutthaya Na Thailand

Peng Liyuan Ta Ziyarci Dakin Adana Kayan Tarihi Na Fasaha Na Birnin Ayutthaya Na Thailand

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.