• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Kudaden Haram Za Su Fuskanci Kalubale Da Sauya Fasalin Kudi —Buhari

by Bello Hamza, Sabo Ahmad and Ibrahim Sabo
3 years ago
in Labarai
0
Masu Kudaden Haram Za Su Fuskanci Kalubale Da Sauya Fasalin Kudi —Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, a ranar Lahadin da ta gabata ya ce matakin da babban bankin Nijeriya (CBN) ya dauka na kaddamar da sabbin kudade da kuma maye gurbinsu da wasu ya samu goyon bayansa kuma yana da yakinin cewa al’umar Nijeriya za su ci riba mai yawa ta yin hakan.

Da yake magana a hirar da wani gidan rediyon Hausa ya yi da fitaccen dan jarida Halilu Ahmed Getso, da Kamaluddeen Sani Shawai da aka gabatar a tashar Tambari TB, Shugaba Buhari ya ce dalilan da CBN suka ba shi sun tabbatar masa da cewa tattalin arzikin kasar zai ci gajiyar yin hakan da kuma samun saukin hauhawar farashin kayan masarufi da magance karakainar jabun kudi da kuma samun karin yawaitar kudaden da ke yawo a cikin Al’uma.

  • Yadda BBC Hausa Ya Karrama Gwarazan Gasar Waƙa Da Hikayata Ta Bana
  • Sake Fasalin Naira: Emefiele Ya Tabbatar Ba Za A Cire Rubutun Ajami Ba – Sanusi 

Ya ce bai dauki tsawon watanni uku na canjin sabbin takardun kudi a matsayin gajeren lokaci ba, saboda idan dai kudin an same su ta hanyar halali hakan ba zai zama damuwa ba.

“Mutanen da ke da kudaden haram da aka binne a karkashin kasa za su fuskanci kalubale da wannan amma ma’aikata da kudaden kasuwanci ba za su fuskanci matsala ba.”

A cikin hirar, shugaban ya kuma yi tsokaci kan batutuwan da suka shafi samar da abinci da tsaron kasa da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Duk lokacin da gwamnati ta fito wanda yake bako ga al’ummar kasa, ko kuma za ta sauya fasalin wani nata, masana a wannan fannin kan yi wa gwamnatin da al’ummar kasa ammfanin wannan tsari ko kuma rashin amfaninsa ga al’ummar kasa.

A wannan karon batun da ya mamaye kasar nan shi maganar canjin kudi, wanda ya zo da rudani. Daga cikin rudanin da aka samu shi ne, cewa, minister kudi da kasafin kudi da tsare-tsaren kasa Zainab Ahmed, ba ta amince da wannan tsarin na sauya fasalin kudin ba.

Shi kuwa, gwamnan babban bankin Nijeriya Godwin Emefele, ana cikin wannan dambarwar ya sanar da cewa, za a sake fasalin akardun kudi na naira 200 da naira 500 da kuma naira 1,000.

Sai dai a wannan dambarwar da ake tsakanin minister da gwamnan babban bankin na Nijerya, shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana karara cewa, ya ba babban bankin Nijeriya cikakken goyon baya na sake fasalin wasau takardun kudin na Nijeriya.

Wani masani tattalin aezikin kasa kuma tsohon manajan nankin Furst Banka da ke Zariya, mai Suna Sani Mamuda Madobi, ya ce, wadanda suka tattara kudin haram masu dimbin yawa, da kuma wasu daga cikin manyatan ‘yansiyasa da suka taskace kudi a wara maboya, ba za su so wannan scanjin kudi ba, saboda kusan kashi 70 daga cikin kasha 100 na kudin nasu, sun boye su ne  Za dai a sauya fasalin naira 200 da naira 500 da kuma naira 1000.

Kamar yadda wasu mutane da dama ke hangen wannan canjin kudi, suna ganin ya zo a daidai lokacin da ya kamata domin ana has ashen cewa, wasu manyan ‘yansiyasa sun taskace kudi, suna jiran a fada kamfen gadan-gadan su yi amfani da su wajen saye ‘yancin jama’a,

Su ma a nasu hangen wasu jam’iyyun na ganin wannan matakin da gwamnati ta dauka, kamar yadda wasu jam’iyyun suka bayyana, babu wanda zai ki wannan shiri na babban bankin na sauya kudi sai dai ‘yansiyasar da ke amfani da makudan kudi wajen saye ‘yancin jama’a.

Sai dai akwai ra’ayi mabambanta daga ‘yan Nijeriya dangane da wanna canjin kudi da za yi. Wadansu na ganin yin hakan zai taimaka wajen saukaka wahalhalun da al’ummar kasar nan ke ciki, domin kuwa dole za ta sa a fito da kudaden da aka boye. Domin da zarar ba a fito da su ba aka canja zuwa sabbin kudin ba har aka rufe canjin sun zama marasa amfani.

Sai dai abu da wani dankasuwa ya lura shi ne, yadda wasu da suka taskace kudin suka fito da su, suna yin ciko kayan amfanin gona da kuma wasu kadarori, wanda hakan ta sa kayan amfanin gonar suka fara tsada tun a wannan lokaci, da ya kamata a ce, suna sauki, yadda talaka zai iya sayen kayan abinci ba tare da fargaba ba.

Saboda haka wasu masu nazari a kan halin rayuwar dan’adam na ganin, duk da wahalar da za a fuskanta a wannan hali, za a warware nan gaba kadan. Kamar yadda suka ce, wannan hanyar na daga cikin hanyoyin da a bi wajen farfado da tattalin arzikin kasar da na al’umma.

Wasu na danganta wahalhalun da ake fuskanta a halin yanzu a wannan kasa da talaucin da ake ciki, da rashin zagayawar kudaden a hannun al’ummar kasa.

Don haka ake ganin wannan mataki da gwamnati da dauka na canjin kudi, zai sa a rage facaka da kudade musamman ga ‘yansiyasa wajen saye ra’ayin mutane.

Kowane abu na da amfani da kuma rashin amfani, sai dai abin da aka fi so shi ne amfanin ya rinjaya, kamar yadda wannan canjin kudin yake, idan aka duba za a ga cewa, amfanin da ke cikinsa ya fi rashin amfanin yawa kamar yadda wasu nasanan suka bayyana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariHaramMasu KudiSauya Fasalin Kudin
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Kungiyar Afenifere Ta Yi Amai Ta Lashe

Next Post

Ganduje Ya Gabatar Da N245.3bn A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Kano 

Related

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

2 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

3 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

3 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

4 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

6 hours ago
Next Post
Ganduje Ya Gabatar Da N245.3bn A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Kano 

Ganduje Ya Gabatar Da N245.3bn A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Kano 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.