ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Kudaden Haram Za Su Fuskanci Kalubale Da Sauya Fasalin Kudi —Buhari

by Bello Hamza, Sabo Ahmad and Ibrahim Sabo
4 years ago
Haram

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, a ranar Lahadin da ta gabata ya ce matakin da babban bankin Nijeriya (CBN) ya dauka na kaddamar da sabbin kudade da kuma maye gurbinsu da wasu ya samu goyon bayansa kuma yana da yakinin cewa al’umar Nijeriya za su ci riba mai yawa ta yin hakan.

Da yake magana a hirar da wani gidan rediyon Hausa ya yi da fitaccen dan jarida Halilu Ahmed Getso, da Kamaluddeen Sani Shawai da aka gabatar a tashar Tambari TB, Shugaba Buhari ya ce dalilan da CBN suka ba shi sun tabbatar masa da cewa tattalin arzikin kasar zai ci gajiyar yin hakan da kuma samun saukin hauhawar farashin kayan masarufi da magance karakainar jabun kudi da kuma samun karin yawaitar kudaden da ke yawo a cikin Al’uma.

  • Yadda BBC Hausa Ya Karrama Gwarazan Gasar Waƙa Da Hikayata Ta Bana
  • Sake Fasalin Naira: Emefiele Ya Tabbatar Ba Za A Cire Rubutun Ajami Ba – Sanusi 

Ya ce bai dauki tsawon watanni uku na canjin sabbin takardun kudi a matsayin gajeren lokaci ba, saboda idan dai kudin an same su ta hanyar halali hakan ba zai zama damuwa ba.

ADVERTISEMENT

“Mutanen da ke da kudaden haram da aka binne a karkashin kasa za su fuskanci kalubale da wannan amma ma’aikata da kudaden kasuwanci ba za su fuskanci matsala ba.”

A cikin hirar, shugaban ya kuma yi tsokaci kan batutuwan da suka shafi samar da abinci da tsaron kasa da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani

Duk lokacin da gwamnati ta fito wanda yake bako ga al’ummar kasa, ko kuma za ta sauya fasalin wani nata, masana a wannan fannin kan yi wa gwamnatin da al’ummar kasa ammfanin wannan tsari ko kuma rashin amfaninsa ga al’ummar kasa.

A wannan karon batun da ya mamaye kasar nan shi maganar canjin kudi, wanda ya zo da rudani. Daga cikin rudanin da aka samu shi ne, cewa, minister kudi da kasafin kudi da tsare-tsaren kasa Zainab Ahmed, ba ta amince da wannan tsarin na sauya fasalin kudin ba.

Shi kuwa, gwamnan babban bankin Nijeriya Godwin Emefele, ana cikin wannan dambarwar ya sanar da cewa, za a sake fasalin akardun kudi na naira 200 da naira 500 da kuma naira 1,000.

Sai dai a wannan dambarwar da ake tsakanin minister da gwamnan babban bankin na Nijerya, shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana karara cewa, ya ba babban bankin Nijeriya cikakken goyon baya na sake fasalin wasau takardun kudin na Nijeriya.

Wani masani tattalin aezikin kasa kuma tsohon manajan nankin Furst Banka da ke Zariya, mai Suna Sani Mamuda Madobi, ya ce, wadanda suka tattara kudin haram masu dimbin yawa, da kuma wasu daga cikin manyatan ‘yansiyasa da suka taskace kudi a wara maboya, ba za su so wannan scanjin kudi ba, saboda kusan kashi 70 daga cikin kasha 100 na kudin nasu, sun boye su ne  Za dai a sauya fasalin naira 200 da naira 500 da kuma naira 1000.

Kamar yadda wasu mutane da dama ke hangen wannan canjin kudi, suna ganin ya zo a daidai lokacin da ya kamata domin ana has ashen cewa, wasu manyan ‘yansiyasa sun taskace kudi, suna jiran a fada kamfen gadan-gadan su yi amfani da su wajen saye ‘yancin jama’a,

Su ma a nasu hangen wasu jam’iyyun na ganin wannan matakin da gwamnati ta dauka, kamar yadda wasu jam’iyyun suka bayyana, babu wanda zai ki wannan shiri na babban bankin na sauya kudi sai dai ‘yansiyasar da ke amfani da makudan kudi wajen saye ‘yancin jama’a.

Sai dai akwai ra’ayi mabambanta daga ‘yan Nijeriya dangane da wanna canjin kudi da za yi. Wadansu na ganin yin hakan zai taimaka wajen saukaka wahalhalun da al’ummar kasar nan ke ciki, domin kuwa dole za ta sa a fito da kudaden da aka boye. Domin da zarar ba a fito da su ba aka canja zuwa sabbin kudin ba har aka rufe canjin sun zama marasa amfani.

Sai dai abu da wani dankasuwa ya lura shi ne, yadda wasu da suka taskace kudin suka fito da su, suna yin ciko kayan amfanin gona da kuma wasu kadarori, wanda hakan ta sa kayan amfanin gonar suka fara tsada tun a wannan lokaci, da ya kamata a ce, suna sauki, yadda talaka zai iya sayen kayan abinci ba tare da fargaba ba.

Saboda haka wasu masu nazari a kan halin rayuwar dan’adam na ganin, duk da wahalar da za a fuskanta a wannan hali, za a warware nan gaba kadan. Kamar yadda suka ce, wannan hanyar na daga cikin hanyoyin da a bi wajen farfado da tattalin arzikin kasar da na al’umma.

Wasu na danganta wahalhalun da ake fuskanta a halin yanzu a wannan kasa da talaucin da ake ciki, da rashin zagayawar kudaden a hannun al’ummar kasa.

Don haka ake ganin wannan mataki da gwamnati da dauka na canjin kudi, zai sa a rage facaka da kudade musamman ga ‘yansiyasa wajen saye ra’ayin mutane.

Kowane abu na da amfani da kuma rashin amfani, sai dai abin da aka fi so shi ne amfanin ya rinjaya, kamar yadda wannan canjin kudin yake, idan aka duba za a ga cewa, amfanin da ke cikinsa ya fi rashin amfanin yawa kamar yadda wasu nasanan suka bayyana.

Haram
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
Haram
Sabo Ahmad
+ posts Bio
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    An Gurfanar Da Mutum 3 Bisa Laifin Lakada Wa Wani Duka Har Lahira
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Tasa Keyar Dakta Idris Dutsen Tanshi Zuwa Gidan Yari
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Uwa Ta Mutu A Kokarin Raba Fada Tsakanin ‘Ya’yanta A Abuja
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    ’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa
Haram
Ibrahim Sabo
+ posts Bio
  • Ibrahim Sabo
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-sabo/
    Sabuwar Hanyar Kwacen Shafin Facebook (II)
  • Ibrahim Sabo
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-sabo/
    Sabuwar Hanyar Kwacen Shafin Facebook (I)
  • Ibrahim Sabo
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-sabo/
    Mene Ne Tsarin 5G?
  • Ibrahim Sabo
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-sabo/
    Yadda Ake Sarrafa Rubutu Ta Word-Processing

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Rahotonni

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani
Labarai

Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani

July 25, 2026
Haram
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Next Post
Ganduje Ya Gabatar Da N245.3bn A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Kano 

Ganduje Ya Gabatar Da N245.3bn A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Kano 

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026
Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

July 25, 2026
Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

July 25, 2026
Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

July 25, 2026
Kalolin Kitso Na Zamani: Yadda Ake Yin Fulani Style

Muhimmancin Kula Da Gashi Domin Lafiyarsa Da Kyawunsa

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.