ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Kudaden Haram Za Su Fuskanci Kalubale Da Sauya Fasalin Kudi —Buhari

by Bello Hamza, Sabo Ahmad and Ibrahim Sabo
4 years ago
Haram

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, a ranar Lahadin da ta gabata ya ce matakin da babban bankin Nijeriya (CBN) ya dauka na kaddamar da sabbin kudade da kuma maye gurbinsu da wasu ya samu goyon bayansa kuma yana da yakinin cewa al’umar Nijeriya za su ci riba mai yawa ta yin hakan.

Da yake magana a hirar da wani gidan rediyon Hausa ya yi da fitaccen dan jarida Halilu Ahmed Getso, da Kamaluddeen Sani Shawai da aka gabatar a tashar Tambari TB, Shugaba Buhari ya ce dalilan da CBN suka ba shi sun tabbatar masa da cewa tattalin arzikin kasar zai ci gajiyar yin hakan da kuma samun saukin hauhawar farashin kayan masarufi da magance karakainar jabun kudi da kuma samun karin yawaitar kudaden da ke yawo a cikin Al’uma.

  • Yadda BBC Hausa Ya Karrama Gwarazan Gasar Waƙa Da Hikayata Ta Bana
  • Sake Fasalin Naira: Emefiele Ya Tabbatar Ba Za A Cire Rubutun Ajami Ba – Sanusi 

Ya ce bai dauki tsawon watanni uku na canjin sabbin takardun kudi a matsayin gajeren lokaci ba, saboda idan dai kudin an same su ta hanyar halali hakan ba zai zama damuwa ba.

ADVERTISEMENT

“Mutanen da ke da kudaden haram da aka binne a karkashin kasa za su fuskanci kalubale da wannan amma ma’aikata da kudaden kasuwanci ba za su fuskanci matsala ba.”

A cikin hirar, shugaban ya kuma yi tsokaci kan batutuwan da suka shafi samar da abinci da tsaron kasa da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Duk lokacin da gwamnati ta fito wanda yake bako ga al’ummar kasa, ko kuma za ta sauya fasalin wani nata, masana a wannan fannin kan yi wa gwamnatin da al’ummar kasa ammfanin wannan tsari ko kuma rashin amfaninsa ga al’ummar kasa.

A wannan karon batun da ya mamaye kasar nan shi maganar canjin kudi, wanda ya zo da rudani. Daga cikin rudanin da aka samu shi ne, cewa, minister kudi da kasafin kudi da tsare-tsaren kasa Zainab Ahmed, ba ta amince da wannan tsarin na sauya fasalin kudin ba.

Shi kuwa, gwamnan babban bankin Nijeriya Godwin Emefele, ana cikin wannan dambarwar ya sanar da cewa, za a sake fasalin akardun kudi na naira 200 da naira 500 da kuma naira 1,000.

Sai dai a wannan dambarwar da ake tsakanin minister da gwamnan babban bankin na Nijerya, shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana karara cewa, ya ba babban bankin Nijeriya cikakken goyon baya na sake fasalin wasau takardun kudin na Nijeriya.

Wani masani tattalin aezikin kasa kuma tsohon manajan nankin Furst Banka da ke Zariya, mai Suna Sani Mamuda Madobi, ya ce, wadanda suka tattara kudin haram masu dimbin yawa, da kuma wasu daga cikin manyatan ‘yansiyasa da suka taskace kudi a wara maboya, ba za su so wannan scanjin kudi ba, saboda kusan kashi 70 daga cikin kasha 100 na kudin nasu, sun boye su ne  Za dai a sauya fasalin naira 200 da naira 500 da kuma naira 1000.

Kamar yadda wasu mutane da dama ke hangen wannan canjin kudi, suna ganin ya zo a daidai lokacin da ya kamata domin ana has ashen cewa, wasu manyan ‘yansiyasa sun taskace kudi, suna jiran a fada kamfen gadan-gadan su yi amfani da su wajen saye ‘yancin jama’a,

Su ma a nasu hangen wasu jam’iyyun na ganin wannan matakin da gwamnati ta dauka, kamar yadda wasu jam’iyyun suka bayyana, babu wanda zai ki wannan shiri na babban bankin na sauya kudi sai dai ‘yansiyasar da ke amfani da makudan kudi wajen saye ‘yancin jama’a.

Sai dai akwai ra’ayi mabambanta daga ‘yan Nijeriya dangane da wanna canjin kudi da za yi. Wadansu na ganin yin hakan zai taimaka wajen saukaka wahalhalun da al’ummar kasar nan ke ciki, domin kuwa dole za ta sa a fito da kudaden da aka boye. Domin da zarar ba a fito da su ba aka canja zuwa sabbin kudin ba har aka rufe canjin sun zama marasa amfani.

Sai dai abu da wani dankasuwa ya lura shi ne, yadda wasu da suka taskace kudin suka fito da su, suna yin ciko kayan amfanin gona da kuma wasu kadarori, wanda hakan ta sa kayan amfanin gonar suka fara tsada tun a wannan lokaci, da ya kamata a ce, suna sauki, yadda talaka zai iya sayen kayan abinci ba tare da fargaba ba.

Saboda haka wasu masu nazari a kan halin rayuwar dan’adam na ganin, duk da wahalar da za a fuskanta a wannan hali, za a warware nan gaba kadan. Kamar yadda suka ce, wannan hanyar na daga cikin hanyoyin da a bi wajen farfado da tattalin arzikin kasar da na al’umma.

Wasu na danganta wahalhalun da ake fuskanta a halin yanzu a wannan kasa da talaucin da ake ciki, da rashin zagayawar kudaden a hannun al’ummar kasa.

Don haka ake ganin wannan mataki da gwamnati da dauka na canjin kudi, zai sa a rage facaka da kudade musamman ga ‘yansiyasa wajen saye ra’ayin mutane.

Kowane abu na da amfani da kuma rashin amfani, sai dai abin da aka fi so shi ne amfanin ya rinjaya, kamar yadda wannan canjin kudin yake, idan aka duba za a ga cewa, amfanin da ke cikinsa ya fi rashin amfanin yawa kamar yadda wasu nasanan suka bayyana.

Haram
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina
Haram
Sabo Ahmad
+ posts Bio
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    An Gurfanar Da Mutum 3 Bisa Laifin Lakada Wa Wani Duka Har Lahira
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Tasa Keyar Dakta Idris Dutsen Tanshi Zuwa Gidan Yari
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Uwa Ta Mutu A Kokarin Raba Fada Tsakanin ‘Ya’yanta A Abuja
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    ’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa
Haram
Ibrahim Sabo
+ posts Bio
  • Ibrahim Sabo
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-sabo/
    Sabuwar Hanyar Kwacen Shafin Facebook (II)
  • Ibrahim Sabo
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-sabo/
    Sabuwar Hanyar Kwacen Shafin Facebook (I)
  • Ibrahim Sabo
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-sabo/
    Mene Ne Tsarin 5G?
  • Ibrahim Sabo
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-sabo/
    Yadda Ake Sarrafa Rubutu Ta Word-Processing

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Ganduje Ya Gabatar Da N245.3bn A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Kano 

Ganduje Ya Gabatar Da N245.3bn A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Kano 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.