• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kungiyar Afenifere Ta Yi Amai Ta Lashe

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
2023: Kungiyar Afenifere Ta Yi Amai Ta Lashe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gamayyar kungiyar Yarbawa zalla ta Afenifere ta yi amai ta lashi, inda a baya ta bayyana cewa tana bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, saboda adalci, bin gaskiya da kuma rashin danne wani sashi na mika mulki ga yankin kudu maso gabasin Nijeriya, amma kuma a yanzu ta bayyana cewa tana goyon bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyatr APC, Bola Ahmed Tinubu a zaben 2023.

Shugabannin kungiyar Afenifere a dukkan fadin yankin kudu maso yamma ciki har da jihohin Kwara da Kogi sun suka bayyana goyan bayan a gidan shugaban kungiyar, Pa Reuben Fasonranti da ke Akure, Babban Birnin Jihar Ondo.

  • Ziyarar Da Shugabar Tanzaniya Za Ta Kawo Sin Za Ta Bunkasa Alaka Tsakanin Kasashen Biyu Zuwa Wani Sabon Matsayi
  • An Cafke Wasu Da Ake Zargi Da Hannu A Mutuwar Mutane Sama Da 130 A Indiya

Sun dai dauki wannan matakin ne bayan ganawa da Tinubu wanda ya ziyarci jihar domin gabatar da manufofinsa na sake fasalin Nijeriya.

Tinubu ya bayyana wa shugabannin Yarbawa cewa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da gwamnonin APC da ke arewa da sauran shugabannin yankin arewa sun yi Imani da cewa shi ne zai iya ceto Nijeriya daga kalubalan da ke fuskanta a halin yanzu.

Da yake gabatar wa shugabannin Yarbawan kundin manufofinsa na samar da ingantacciyar Nijeriya, Tinubu ya jaddada musu cewa za a samu ingantacciyar Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

Idan za a iya tunawa dai lokacin da ya ziyarci Pa Fasoranti a ranar 4 ga watan Maris na wannan shekara kafin zaben fid da gwani na jam’iyyar APC, Tinubu ya yi wa shugaban kungiyar Afenifere alkawarin cewa zai dawo a lokacin da ya samu tikitin takarar shugaban kasa.

Tinubu ya ce ya zo Ondo ne domin ya cika alkawarin da ya dauka a baya, inda ya bukaci shugabannin Yarbawan su gode wa Shugaba Buhari da gwamnonin arewa bisa ba shi dama a jam’iyyarn APC.

Tsohon gwamna Jihar Legas ya ce, “’Yan arewa sun tabbatar mun da cewa zan iya hada kan Nijeriya. Wasu sun yi kokarin zuwa wurin Shugaban kasa Muhammadu Buhari domin gabatar da wani, amma shugaban ya ki amincewa da bukatarsu, inda ya dage sai an bi tsarin yadda dimokuradiyya ya shimfida. Shugaban ya ce duk wanda zai daga martabar jam’iyyar APC shi ne ya cancanta. Daga baya dai ya karkara zuwa ga gaskiya.

“Gwamnonin APC na arewa su suka dage dole sai mulki ya je yankin kudu, musamman ma kudu maso yamma. Gwamna Nasir El-Rufai da Abdullahi Ganduje da sauransu su suka goya min baya daga karshe,” in ji Tinubu.

Tun da farko dai, sakatare janar na kungiyar Afenifere, Cif Seinde Arogbofa ya bukaci Tinubu ya zama shugaban kasa domin hada kan Nijeriya da aiki tukuru wajen inganta kasa baki daya.

Ya ce, “Ba wai za ka kasance shugaban Yarbawa ba ne kadai, sai dai shugaban Nijeriya gaba daya. Lokacin da ka zama shugaban kasa, duk abin da za ka yi ka dunga tunawa da Nijeriya sannan kar ka manta da gida. Ka san irin bukatocinmu wadanda suka hada da samar da tsaro da inganta tattalin arziki. A yanzu haka kasarmu babu tsaro, muna bukatar ‘yansandan jihohi saboda tsaron kasarmu.”

Mataimakin gwamnan Jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa wanda shi ne ya tarbi Tinubu a madadin Gwamna Rotimi Akeredolu ya bayyana cewa, mutanen Jihar Ondo da kungiyar Afenifere suna goyon bayan Tinubu ya zama shugaban kasa.

Sakamakon ganawar kungiyar Afenifere da Tinubu, mai magana da yawun tawagar yakin neman zaben Atiku/Okowa, Daniel Bwala ya bayyana cewa kamata ya yi kungiyar Afenifere ta gayyaci sauran manyan ‘yan takarar shugaban kasa a zaben 2023 ba wai na APC kadai ba.

“Na yi tsammanin Afenifere za ta gayyaci manyan ‘yan takara guda hudu kamar yadda kungiyar arewa ta yi, amma sai ta gayyaci Tinubu kawai,” in ji shi.

Da yake mayar da martani game da goyon bayan Tinubu, Bwala ya ce kasancewa rashin halartar ganawar da wasu jiga-jigan ‘yan kungiyan kamar irinsu Pa Ayo Adebanjo da Cif Sola Ebiseni ya nuna goyon ba halattacce ba ne.

Bwala ya siffanta Tinubu a matsayin wanda yake kokarin amfani da kabilanci domin ya samu nasara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmaiKungiyaLAshewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadari Gabas… Tsugune Ba Ta Kare Ba A  Jam’iyyar PDP

Next Post

Masu Kudaden Haram Za Su Fuskanci Kalubale Da Sauya Fasalin Kudi —Buhari

Related

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC
Labarai

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

9 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

10 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

11 hours ago
Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

12 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

Lauyoyin Majalisar Dattawa Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki

14 hours ago
Namadi Sambo Ya Yaba Wa Gwamna Abba Yusuf Kan Bunƙasa Ɓangaren Ilimi Da Gine-Gine A Kano
Manyan Labarai

Namadi Sambo Ya Yaba Wa Gwamna Abba Yusuf Kan Bunƙasa Ɓangaren Ilimi Da Gine-Gine A Kano

15 hours ago
Next Post
Masu Kudaden Haram Za Su Fuskanci Kalubale Da Sauya Fasalin Kudi —Buhari

Masu Kudaden Haram Za Su Fuskanci Kalubale Da Sauya Fasalin Kudi —Buhari

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.