ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kungiyar Afenifere Ta Yi Amai Ta Lashe

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Lashe

Gamayyar kungiyar Yarbawa zalla ta Afenifere ta yi amai ta lashi, inda a baya ta bayyana cewa tana bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, saboda adalci, bin gaskiya da kuma rashin danne wani sashi na mika mulki ga yankin kudu maso gabasin Nijeriya, amma kuma a yanzu ta bayyana cewa tana goyon bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyatr APC, Bola Ahmed Tinubu a zaben 2023.

Shugabannin kungiyar Afenifere a dukkan fadin yankin kudu maso yamma ciki har da jihohin Kwara da Kogi sun suka bayyana goyan bayan a gidan shugaban kungiyar, Pa Reuben Fasonranti da ke Akure, Babban Birnin Jihar Ondo.

  • Ziyarar Da Shugabar Tanzaniya Za Ta Kawo Sin Za Ta Bunkasa Alaka Tsakanin Kasashen Biyu Zuwa Wani Sabon Matsayi
  • An Cafke Wasu Da Ake Zargi Da Hannu A Mutuwar Mutane Sama Da 130 A Indiya

Sun dai dauki wannan matakin ne bayan ganawa da Tinubu wanda ya ziyarci jihar domin gabatar da manufofinsa na sake fasalin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Tinubu ya bayyana wa shugabannin Yarbawa cewa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da gwamnonin APC da ke arewa da sauran shugabannin yankin arewa sun yi Imani da cewa shi ne zai iya ceto Nijeriya daga kalubalan da ke fuskanta a halin yanzu.

Da yake gabatar wa shugabannin Yarbawan kundin manufofinsa na samar da ingantacciyar Nijeriya, Tinubu ya jaddada musu cewa za a samu ingantacciyar Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Idan za a iya tunawa dai lokacin da ya ziyarci Pa Fasoranti a ranar 4 ga watan Maris na wannan shekara kafin zaben fid da gwani na jam’iyyar APC, Tinubu ya yi wa shugaban kungiyar Afenifere alkawarin cewa zai dawo a lokacin da ya samu tikitin takarar shugaban kasa.

Tinubu ya ce ya zo Ondo ne domin ya cika alkawarin da ya dauka a baya, inda ya bukaci shugabannin Yarbawan su gode wa Shugaba Buhari da gwamnonin arewa bisa ba shi dama a jam’iyyarn APC.

Tsohon gwamna Jihar Legas ya ce, “’Yan arewa sun tabbatar mun da cewa zan iya hada kan Nijeriya. Wasu sun yi kokarin zuwa wurin Shugaban kasa Muhammadu Buhari domin gabatar da wani, amma shugaban ya ki amincewa da bukatarsu, inda ya dage sai an bi tsarin yadda dimokuradiyya ya shimfida. Shugaban ya ce duk wanda zai daga martabar jam’iyyar APC shi ne ya cancanta. Daga baya dai ya karkara zuwa ga gaskiya.

“Gwamnonin APC na arewa su suka dage dole sai mulki ya je yankin kudu, musamman ma kudu maso yamma. Gwamna Nasir El-Rufai da Abdullahi Ganduje da sauransu su suka goya min baya daga karshe,” in ji Tinubu.

Tun da farko dai, sakatare janar na kungiyar Afenifere, Cif Seinde Arogbofa ya bukaci Tinubu ya zama shugaban kasa domin hada kan Nijeriya da aiki tukuru wajen inganta kasa baki daya.

Ya ce, “Ba wai za ka kasance shugaban Yarbawa ba ne kadai, sai dai shugaban Nijeriya gaba daya. Lokacin da ka zama shugaban kasa, duk abin da za ka yi ka dunga tunawa da Nijeriya sannan kar ka manta da gida. Ka san irin bukatocinmu wadanda suka hada da samar da tsaro da inganta tattalin arziki. A yanzu haka kasarmu babu tsaro, muna bukatar ‘yansandan jihohi saboda tsaron kasarmu.”

Mataimakin gwamnan Jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa wanda shi ne ya tarbi Tinubu a madadin Gwamna Rotimi Akeredolu ya bayyana cewa, mutanen Jihar Ondo da kungiyar Afenifere suna goyon bayan Tinubu ya zama shugaban kasa.

Sakamakon ganawar kungiyar Afenifere da Tinubu, mai magana da yawun tawagar yakin neman zaben Atiku/Okowa, Daniel Bwala ya bayyana cewa kamata ya yi kungiyar Afenifere ta gayyaci sauran manyan ‘yan takarar shugaban kasa a zaben 2023 ba wai na APC kadai ba.

“Na yi tsammanin Afenifere za ta gayyaci manyan ‘yan takara guda hudu kamar yadda kungiyar arewa ta yi, amma sai ta gayyaci Tinubu kawai,” in ji shi.

Da yake mayar da martani game da goyon bayan Tinubu, Bwala ya ce kasancewa rashin halartar ganawar da wasu jiga-jigan ‘yan kungiyan kamar irinsu Pa Ayo Adebanjo da Cif Sola Ebiseni ya nuna goyon ba halattacce ba ne.

Bwala ya siffanta Tinubu a matsayin wanda yake kokarin amfani da kabilanci domin ya samu nasara.

Lashe
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Masu Kudaden Haram Za Su Fuskanci Kalubale Da Sauya Fasalin Kudi —Buhari

Masu Kudaden Haram Za Su Fuskanci Kalubale Da Sauya Fasalin Kudi —Buhari

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.