• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Kwacen Waya Sun Kashe Dattijuwa A Gombe

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Masu Kwacen Waya Sun Kashe Dattijuwa A Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu masu kwacen waya sun hallaka wata mata ‘yar shekara 58 a duniya, Aishatu Abdullahi, a gidanta da ke Jeka Da Fari ta jihar Gombe a daren ranar Juma’a. 

An ruwaito cewa ‘yan daban sun mamaye gidan marigayiyar da misalin karfe 9:45 na dare domin yi mata fashi da makami.

  • Rusau: Kotu Ta Gargadi Gwamnatin Kano Kan Rashin Bin Umarninta
  • Da Kyar Nake Samun Yin Sallah Sakamakon Yawan Mutane Masu Korafi – El-Mustapha

A kokarin da suke yi na mata fashin wayar ne suka daba mata wuka da ya yi sanadiyyar ajalinta.

Lamarin da ya tada hankalin al’ummar unguwar.

Idan za a tuna dai a ‘yan watannin baya kadan wasu ‘yan daba sun shiga gidan fitaccen malamin addinin musulumci da ke jihar, Sheikh Albani Kuri, da manufar masa fashin wayoyi daga baya ma suka kashe shi sakamakon kin ba su wayoyin nasa.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Rundunar ‘yansandan jihar Gombe ta mika ta’aziyyarta da jimami dangane da kisan matar, inda ta sha alwashin binciko makasan a duk inda suke domin wanzar da adalci a tsakani.

A wata sanarwa dauke da sanya hannun kakakin rundunar ‘yansandan jihar, Mahid Muazu Abubakar, da ya fitar a ranar Asabar, ta ce za su kamo makasan babu makawa.

Ya ce, “Kwamishinan ‘yansanda mai kula da sashen ayyuka na jihar Gombe CP Hayatu Usman a madadin kwamishinan ‘yansandan jihar Gombe ya umarci mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da ya tsaurara bincike kan kisan da aka yi wa Aishatu Abdullahi a ranar Juma’a.

“Bayan samun labarin faruwar lamarin, jami’an ‘yansanda sun ziyarci wurin da lamarin ya faru inda aka samu gawar Aisha kwance cikin jini, nan take aka garzaya da ita asibitin kwararru, a nan ne aka tabbatar da mutuwarta.”

Rundunar ta roki jama’a da su taimaka mata da bayanan yadda za a cafko makasan da sauran ayyukan ta’addanci a jihar.

Shi ma, gwamnan jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi tir da Allah wadai da kisan matar.

A wata sanarwa dauke da sanya hannun babban hadimin gwamnan a bangaren yada labarai, Isma’ila Uba Misilli, gwamnan ya umarci jami’an tsaro da su gaggauta kamo makasan.

Ya mika ta’aziyyarsa da addu’ar Allah jikan mamaciyar.

Gwamnan ya tabbatar da cewa ba za su taba bari jininta ya tafi a banza ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rusau: Kotu Ta Gargadi Gwamnatin Kano Kan Rashin Bin Umarninta

Next Post

Xi Ya Aika Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 110 Da Kafuwar Kungiyar Daliban Sin Dake Turai Da Amurka

Related

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

5 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

6 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

7 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

8 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

10 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

11 hours ago
Next Post
Xi Ya Aika Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 110 Da Kafuwar Kungiyar Daliban Sin Dake Turai Da Amurka

Xi Ya Aika Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 110 Da Kafuwar Kungiyar Daliban Sin Dake Turai Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.