• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Kwacen Waya Sun Kashe Dattijuwa A Gombe

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Masu Kwacen Waya Sun Kashe Dattijuwa A Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu masu kwacen waya sun hallaka wata mata ‘yar shekara 58 a duniya, Aishatu Abdullahi, a gidanta da ke Jeka Da Fari ta jihar Gombe a daren ranar Juma’a. 

An ruwaito cewa ‘yan daban sun mamaye gidan marigayiyar da misalin karfe 9:45 na dare domin yi mata fashi da makami.

  • Rusau: Kotu Ta Gargadi Gwamnatin Kano Kan Rashin Bin Umarninta
  • Da Kyar Nake Samun Yin Sallah Sakamakon Yawan Mutane Masu Korafi – El-Mustapha

A kokarin da suke yi na mata fashin wayar ne suka daba mata wuka da ya yi sanadiyyar ajalinta.

Lamarin da ya tada hankalin al’ummar unguwar.

Idan za a tuna dai a ‘yan watannin baya kadan wasu ‘yan daba sun shiga gidan fitaccen malamin addinin musulumci da ke jihar, Sheikh Albani Kuri, da manufar masa fashin wayoyi daga baya ma suka kashe shi sakamakon kin ba su wayoyin nasa.

Labarai Masu Nasaba

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Rundunar ‘yansandan jihar Gombe ta mika ta’aziyyarta da jimami dangane da kisan matar, inda ta sha alwashin binciko makasan a duk inda suke domin wanzar da adalci a tsakani.

A wata sanarwa dauke da sanya hannun kakakin rundunar ‘yansandan jihar, Mahid Muazu Abubakar, da ya fitar a ranar Asabar, ta ce za su kamo makasan babu makawa.

Ya ce, “Kwamishinan ‘yansanda mai kula da sashen ayyuka na jihar Gombe CP Hayatu Usman a madadin kwamishinan ‘yansandan jihar Gombe ya umarci mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da ya tsaurara bincike kan kisan da aka yi wa Aishatu Abdullahi a ranar Juma’a.

“Bayan samun labarin faruwar lamarin, jami’an ‘yansanda sun ziyarci wurin da lamarin ya faru inda aka samu gawar Aisha kwance cikin jini, nan take aka garzaya da ita asibitin kwararru, a nan ne aka tabbatar da mutuwarta.”

Rundunar ta roki jama’a da su taimaka mata da bayanan yadda za a cafko makasan da sauran ayyukan ta’addanci a jihar.

Shi ma, gwamnan jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi tir da Allah wadai da kisan matar.

A wata sanarwa dauke da sanya hannun babban hadimin gwamnan a bangaren yada labarai, Isma’ila Uba Misilli, gwamnan ya umarci jami’an tsaro da su gaggauta kamo makasan.

Ya mika ta’aziyyarsa da addu’ar Allah jikan mamaciyar.

Gwamnan ya tabbatar da cewa ba za su taba bari jininta ya tafi a banza ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rusau: Kotu Ta Gargadi Gwamnatin Kano Kan Rashin Bin Umarninta

Next Post

Xi Ya Aika Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 110 Da Kafuwar Kungiyar Daliban Sin Dake Turai Da Amurka

Related

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

4 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

5 hours ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

6 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

8 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

11 hours ago
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
Labarai

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

20 hours ago
Next Post
Xi Ya Aika Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 110 Da Kafuwar Kungiyar Daliban Sin Dake Turai Da Amurka

Xi Ya Aika Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 110 Da Kafuwar Kungiyar Daliban Sin Dake Turai Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An ÆŠaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An ÆŠaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.