• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Kwacen Waya Sun Kashe Dattijuwa A Gombe

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Masu Kwacen Waya Sun Kashe Dattijuwa A Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu masu kwacen waya sun hallaka wata mata ‘yar shekara 58 a duniya, Aishatu Abdullahi, a gidanta da ke Jeka Da Fari ta jihar Gombe a daren ranar Juma’a. 

An ruwaito cewa ‘yan daban sun mamaye gidan marigayiyar da misalin karfe 9:45 na dare domin yi mata fashi da makami.

  • Rusau: Kotu Ta Gargadi Gwamnatin Kano Kan Rashin Bin Umarninta
  • Da Kyar Nake Samun Yin Sallah Sakamakon Yawan Mutane Masu Korafi – El-Mustapha

A kokarin da suke yi na mata fashin wayar ne suka daba mata wuka da ya yi sanadiyyar ajalinta.

Lamarin da ya tada hankalin al’ummar unguwar.

Idan za a tuna dai a ‘yan watannin baya kadan wasu ‘yan daba sun shiga gidan fitaccen malamin addinin musulumci da ke jihar, Sheikh Albani Kuri, da manufar masa fashin wayoyi daga baya ma suka kashe shi sakamakon kin ba su wayoyin nasa.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Rundunar ‘yansandan jihar Gombe ta mika ta’aziyyarta da jimami dangane da kisan matar, inda ta sha alwashin binciko makasan a duk inda suke domin wanzar da adalci a tsakani.

A wata sanarwa dauke da sanya hannun kakakin rundunar ‘yansandan jihar, Mahid Muazu Abubakar, da ya fitar a ranar Asabar, ta ce za su kamo makasan babu makawa.

Ya ce, “Kwamishinan ‘yansanda mai kula da sashen ayyuka na jihar Gombe CP Hayatu Usman a madadin kwamishinan ‘yansandan jihar Gombe ya umarci mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da ya tsaurara bincike kan kisan da aka yi wa Aishatu Abdullahi a ranar Juma’a.

“Bayan samun labarin faruwar lamarin, jami’an ‘yansanda sun ziyarci wurin da lamarin ya faru inda aka samu gawar Aisha kwance cikin jini, nan take aka garzaya da ita asibitin kwararru, a nan ne aka tabbatar da mutuwarta.”

Rundunar ta roki jama’a da su taimaka mata da bayanan yadda za a cafko makasan da sauran ayyukan ta’addanci a jihar.

Shi ma, gwamnan jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi tir da Allah wadai da kisan matar.

A wata sanarwa dauke da sanya hannun babban hadimin gwamnan a bangaren yada labarai, Isma’ila Uba Misilli, gwamnan ya umarci jami’an tsaro da su gaggauta kamo makasan.

Ya mika ta’aziyyarsa da addu’ar Allah jikan mamaciyar.

Gwamnan ya tabbatar da cewa ba za su taba bari jininta ya tafi a banza ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rusau: Kotu Ta Gargadi Gwamnatin Kano Kan Rashin Bin Umarninta

Next Post

Xi Ya Aika Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 110 Da Kafuwar Kungiyar Daliban Sin Dake Turai Da Amurka

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

3 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

4 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

5 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

9 hours ago
Gombe
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

10 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

11 hours ago
Next Post
Xi Ya Aika Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 110 Da Kafuwar Kungiyar Daliban Sin Dake Turai Da Amurka

Xi Ya Aika Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 110 Da Kafuwar Kungiyar Daliban Sin Dake Turai Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.