ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Kwacen Waya Sun Kashe Dattijuwa A Gombe

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gombe

Wasu masu kwacen waya sun hallaka wata mata ‘yar shekara 58 a duniya, Aishatu Abdullahi, a gidanta da ke Jeka Da Fari ta jihar Gombe a daren ranar Juma’a. 

An ruwaito cewa ‘yan daban sun mamaye gidan marigayiyar da misalin karfe 9:45 na dare domin yi mata fashi da makami.

  • Rusau: Kotu Ta Gargadi Gwamnatin Kano Kan Rashin Bin Umarninta
  • Da Kyar Nake Samun Yin Sallah Sakamakon Yawan Mutane Masu Korafi – El-Mustapha

A kokarin da suke yi na mata fashin wayar ne suka daba mata wuka da ya yi sanadiyyar ajalinta.

ADVERTISEMENT

Lamarin da ya tada hankalin al’ummar unguwar.

Idan za a tuna dai a ‘yan watannin baya kadan wasu ‘yan daba sun shiga gidan fitaccen malamin addinin musulumci da ke jihar, Sheikh Albani Kuri, da manufar masa fashin wayoyi daga baya ma suka kashe shi sakamakon kin ba su wayoyin nasa.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Rundunar ‘yansandan jihar Gombe ta mika ta’aziyyarta da jimami dangane da kisan matar, inda ta sha alwashin binciko makasan a duk inda suke domin wanzar da adalci a tsakani.

A wata sanarwa dauke da sanya hannun kakakin rundunar ‘yansandan jihar, Mahid Muazu Abubakar, da ya fitar a ranar Asabar, ta ce za su kamo makasan babu makawa.

Ya ce, “Kwamishinan ‘yansanda mai kula da sashen ayyuka na jihar Gombe CP Hayatu Usman a madadin kwamishinan ‘yansandan jihar Gombe ya umarci mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da ya tsaurara bincike kan kisan da aka yi wa Aishatu Abdullahi a ranar Juma’a.

“Bayan samun labarin faruwar lamarin, jami’an ‘yansanda sun ziyarci wurin da lamarin ya faru inda aka samu gawar Aisha kwance cikin jini, nan take aka garzaya da ita asibitin kwararru, a nan ne aka tabbatar da mutuwarta.”

Rundunar ta roki jama’a da su taimaka mata da bayanan yadda za a cafko makasan da sauran ayyukan ta’addanci a jihar.

Shi ma, gwamnan jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi tir da Allah wadai da kisan matar.

A wata sanarwa dauke da sanya hannun babban hadimin gwamnan a bangaren yada labarai, Isma’ila Uba Misilli, gwamnan ya umarci jami’an tsaro da su gaggauta kamo makasan.

Ya mika ta’aziyyarsa da addu’ar Allah jikan mamaciyar.

Gwamnan ya tabbatar da cewa ba za su taba bari jininta ya tafi a banza ba.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Xi Ya Aika Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 110 Da Kafuwar Kungiyar Daliban Sin Dake Turai Da Amurka

Xi Ya Aika Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 110 Da Kafuwar Kungiyar Daliban Sin Dake Turai Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.