• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Muguwar Niyya Ba Za Su Samu Biyan Bukata Ba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Masu Muguwar Niyya Ba Za Su Samu Biyan Bukata Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 1 ga watan Yuli mai kamawa rana ce ta cika shekaru 25 da yankin Hong Kong na kasar Sin ya koma gida. Da ma a karni na 19, kasar Birtaniya ta kwaci yankin daga kasar Sin, har ma ta yi shekaru fiye da 100 tana mulkin mallaka a can, kafin daga bisani sabuwar kasar Sin ta sanya Birtaniya mayar da yankin, a shekarar 1997, ta hanyar dokoki da shawarwari.

Amma kun san halayyar ‘yan mulkin mallaka. Kafin su bar wani wuri, to, dole ne su ta da rikici can, ta yadda za su ci gaba da yin tasiri a wurin nan gaba.

Wannan batu dalili ne da ya sa ake samun rikicin kabilu a Najeriya, da kiyayar da ake samu tsakanin India da Pakistan, da dai sauran rikice-rikice daban daban, ciki har da wasu matsalolin da suka shafi yankin Hong Kong na kasar Sin.

Cikin shekaru fiye da 100 da Birtaniya take mulkin mallaka a Hong Kong, ba ta taba ba mutanen wurin hakkin dimokuradiya ba. Duk da haka, a shekarun 1990, wato dab da lokacin dawowar yankin Hong Kong karkashin mulkin kasar Sin, Birtaniya ta fara aiwatar da tsarin dimokuradiyya a Hong Kong, don neman samun rarrabuwar kawuna a fannin siyasa tsakanin al’ummun wurin, da kawo cikas ga mulkin da gwamnatin kasar Sin za ta gudanar a yankin Hong Kong.

Sa’an nan Birtaniya ta taimaki mutanen yankin Hong Kong masu kishinta wajen zama manyan jami’ai da masu fada a ji, musamman ma a bangaren aikin ilimi da al’adu.

Labarai Masu Nasaba

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Ban da haka, Birtaniya ta yi hadin gwiwa da Amurka a kokarin sauya tunanin mutanen yankin Hong Kong. Misali, cikin littafin da kasar Birtaniya ta gabatar dangane da tarihin yankin Hong Kong, an bayyana isowar ‘yan Birtaniya a yankin a shekarar 1841 a matsayin mafarin tarihin yankin Hong Kong, ba tare da lura da alakar dake tsakanin yankin da kasa mahaifa ta Sin, wadda ke da tarihi na shekaru 5000 ba. Kana a nata bangare, kasar Amurka ta tallafi wasu hukumomi, ta “Asusun raya dimokuradiyya NED”, wadanda suka tsara littattafan karatun da aka yi amfani da su cikin jami’o’i 8 dake Hong Kong. Ta wannan hanya an dasa tunani na “kin jinin gwamnatin Sin” da “balle yankin Hong Kong” cikin kwakwalwar daliban jami’a.

Makarkashiyar siyasa da Amurka da Birtaniya suka kulla ta haifar da mummunan sakamako a shekarar 2019, inda aka samu zanga-zanga da bore a yankin Hong Kong, yanayin da ya dade har tsawon rabin shekara kafin a shawo kansa, wanda ya yi barna sosai ga al’ummar Hong Kong. Duk da haka, shugabannin kasashen Amurka da Birtaniya sun mara wa ‘yan bore baya, kana dimbin hukumomin kasar Amurka sun samar musu da tallafi, gami da ba su horo cikin wani dogon lokaci.

Ko da yake kasashen Birtaniya da Amurka sun yi kokarin ta da zaune-tsaye a yankin Hong Kong, amma kura ta lafa a yankin tun tuni, inda aka dawo da kwanciyar hankali. Dalilin da ya sa haka, shi ne domin gwamnatin kasar Sin ta dauki kwararran matakai na daidaita yanayin Hong Kong, inda ta gabatar da dokar tsaron kasa a Hong Hong, da daidaita tsarin zabe na yankin, don tabbatar da ganin cewa za a ba mutane masu kishin kasa damar gudanar da mulki. Ban da haka, an dauki matakai na karfafa tunanin al’umma na kasancewarsu ‘yan kasa. Sa’an nan wani dalili na daban da ya sa ake iya kwantar da kurar da ta tashi a Hong Kong, shi ne domin misalan wasu kasashen da aka gudanar da bore na neman juyin juya hali, irinsu Syria, da Libya, da Ukraine, sun sa al’umma fahimtar cewa ana neman ta da zaune tsaye don neman raunana yankin Hong Kong da kasar Sin baki daya kawai, maimakon kare hakkin jama’ar Hong Kong.

A nan za mu iya ganin cewa, ko da yake su kasashen Amurka da Birtaniya sun dade suna kokarin ta da rikici a yankin Hong Kong, amma a karshe dai, sun kasa samun biyan bukata, hakan ma ya nuna karfin al’ummar kasar Sin wajen kare kasarsu. Duk wata makarkashiyar da aka kulla ta neman raunana kasar Sin ba za ta samu nasara ba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Bene Mai Hawa Uku Ya Ruguje A Fatakwal

Next Post

Babu Abin Da Zai Bata Sunan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

Related

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya
Daga Birnin Sin

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

5 hours ago
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

7 hours ago
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 
Daga Birnin Sin

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

7 hours ago
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya
Daga Birnin Sin

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

9 hours ago
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

9 hours ago
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

12 hours ago
Next Post
Babu Abin Da Zai Bata Sunan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

Babu Abin Da Zai Bata Sunan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

LABARAI MASU NASABA

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.