ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Muguwar Niyya Ba Za Su Samu Biyan Bukata Ba

by CMG Hausa
4 years ago

Ranar 1 ga watan Yuli mai kamawa rana ce ta cika shekaru 25 da yankin Hong Kong na kasar Sin ya koma gida. Da ma a karni na 19, kasar Birtaniya ta kwaci yankin daga kasar Sin, har ma ta yi shekaru fiye da 100 tana mulkin mallaka a can, kafin daga bisani sabuwar kasar Sin ta sanya Birtaniya mayar da yankin, a shekarar 1997, ta hanyar dokoki da shawarwari.

Amma kun san halayyar ‘yan mulkin mallaka. Kafin su bar wani wuri, to, dole ne su ta da rikici can, ta yadda za su ci gaba da yin tasiri a wurin nan gaba.

Wannan batu dalili ne da ya sa ake samun rikicin kabilu a Najeriya, da kiyayar da ake samu tsakanin India da Pakistan, da dai sauran rikice-rikice daban daban, ciki har da wasu matsalolin da suka shafi yankin Hong Kong na kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Cikin shekaru fiye da 100 da Birtaniya take mulkin mallaka a Hong Kong, ba ta taba ba mutanen wurin hakkin dimokuradiya ba. Duk da haka, a shekarun 1990, wato dab da lokacin dawowar yankin Hong Kong karkashin mulkin kasar Sin, Birtaniya ta fara aiwatar da tsarin dimokuradiyya a Hong Kong, don neman samun rarrabuwar kawuna a fannin siyasa tsakanin al’ummun wurin, da kawo cikas ga mulkin da gwamnatin kasar Sin za ta gudanar a yankin Hong Kong.

Sa’an nan Birtaniya ta taimaki mutanen yankin Hong Kong masu kishinta wajen zama manyan jami’ai da masu fada a ji, musamman ma a bangaren aikin ilimi da al’adu.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Ban da haka, Birtaniya ta yi hadin gwiwa da Amurka a kokarin sauya tunanin mutanen yankin Hong Kong. Misali, cikin littafin da kasar Birtaniya ta gabatar dangane da tarihin yankin Hong Kong, an bayyana isowar ‘yan Birtaniya a yankin a shekarar 1841 a matsayin mafarin tarihin yankin Hong Kong, ba tare da lura da alakar dake tsakanin yankin da kasa mahaifa ta Sin, wadda ke da tarihi na shekaru 5000 ba. Kana a nata bangare, kasar Amurka ta tallafi wasu hukumomi, ta “Asusun raya dimokuradiyya NED”, wadanda suka tsara littattafan karatun da aka yi amfani da su cikin jami’o’i 8 dake Hong Kong. Ta wannan hanya an dasa tunani na “kin jinin gwamnatin Sin” da “balle yankin Hong Kong” cikin kwakwalwar daliban jami’a.

Makarkashiyar siyasa da Amurka da Birtaniya suka kulla ta haifar da mummunan sakamako a shekarar 2019, inda aka samu zanga-zanga da bore a yankin Hong Kong, yanayin da ya dade har tsawon rabin shekara kafin a shawo kansa, wanda ya yi barna sosai ga al’ummar Hong Kong. Duk da haka, shugabannin kasashen Amurka da Birtaniya sun mara wa ‘yan bore baya, kana dimbin hukumomin kasar Amurka sun samar musu da tallafi, gami da ba su horo cikin wani dogon lokaci.

Ko da yake kasashen Birtaniya da Amurka sun yi kokarin ta da zaune-tsaye a yankin Hong Kong, amma kura ta lafa a yankin tun tuni, inda aka dawo da kwanciyar hankali. Dalilin da ya sa haka, shi ne domin gwamnatin kasar Sin ta dauki kwararran matakai na daidaita yanayin Hong Kong, inda ta gabatar da dokar tsaron kasa a Hong Hong, da daidaita tsarin zabe na yankin, don tabbatar da ganin cewa za a ba mutane masu kishin kasa damar gudanar da mulki. Ban da haka, an dauki matakai na karfafa tunanin al’umma na kasancewarsu ‘yan kasa. Sa’an nan wani dalili na daban da ya sa ake iya kwantar da kurar da ta tashi a Hong Kong, shi ne domin misalan wasu kasashen da aka gudanar da bore na neman juyin juya hali, irinsu Syria, da Libya, da Ukraine, sun sa al’umma fahimtar cewa ana neman ta da zaune tsaye don neman raunana yankin Hong Kong da kasar Sin baki daya kawai, maimakon kare hakkin jama’ar Hong Kong.

A nan za mu iya ganin cewa, ko da yake su kasashen Amurka da Birtaniya sun dade suna kokarin ta da rikici a yankin Hong Kong, amma a karshe dai, sun kasa samun biyan bukata, hakan ma ya nuna karfin al’ummar kasar Sin wajen kare kasarsu. Duk wata makarkashiyar da aka kulla ta neman raunana kasar Sin ba za ta samu nasara ba. (Bello Wang)

CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Babu Abin Da Zai Bata Sunan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

Babu Abin Da Zai Bata Sunan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.