• Leadership Hausa
Monday, October 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Abin Da Zai Bata Sunan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

by CMG Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Babu Abin Da Zai Bata Sunan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A duk lokacin da aka bullo da wata manufa ko hadin gwiwa da nufin inganta rayuwar al’ummomin kasashen duniya, ya kamata kowa ya ga sakamakon hakan a zahiri, kamar yadda shawarar “ziri daya da hanya daya” ta samarwa kasashen da ke cikinta da ma hadin gwiwar kasashen Sin da Afirka da ya haifar da gagarumin sakamakon, sabanin yadda Amurka da kawayenta ke neman bata sunan shawarar yayin taron G7 na baya-bayan da suka gudanar a kasar Jamus.

Sai dai duk wani surutu da Amurka da masu neman bata sunan shawarar za su yi, hakarsu ba za ta cimma ruwa ba, domin kan Mage ya riga ya waye, galibin kasashen da suka amfana da shawarar, ba za su taba yarda a yi musu sakiyar da babu ruwa ba.

Har kullum kasar Sin wadda ta gabatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, tana maraba da duk wata shawarar da za ta inganta muhimman ababen more rayuwar al’ummar duniya. A hannu guda kuma, tana nuna adawa ga duk wani yunkuri na bata sunan shawarar “ziri daya da hanya daya”, bisa hujjar inganta muhimman ababen more rayuwar al’umma, don cimma wani muradun siyasa.

Wannan batu na zuwa ne, yayin da shugaban Amurka Joe Bide a wajen taron kolin kasashen G7, ya sanar da kaddamar da wai, wani shirin hadin gwiwa kan inganta muhimman ababen more rayuwar al’umma da zuba jari a duniya”, har ma wasu manyan jami’an gwamnatin Amurka da ba’a san ko su waye ba, sun rika furta kalamai na shafawa shawarar “ziri daya da hanya daya” ta kasar Sin bakin fenti. Duniya ta sha jin surutu da alkawura daga bangaren Amurka ba tare da cikawa ba.

Wani abin takaici ma shi ne, wai kasar da ba ta wadatu da ababen more rayuwa a cikin gidan ta ba , ita ce za ta jagoranci aiwatar da abin da ake kira ayyukan samar da ababen more rayuwa a duniya. Amma idan mutum ya ce, zai ba ka riga to ka kalli ta wuyansa.

Labarai Masu Nasaba

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

Idan ba a manta ba, a yayin taron G7 da aka gudanar a shekarar da ta gabata, an bijiro da maganar shawarar hadin gwiwa da ake kira “Sake gina duniya mai kyau” (B3W), tare da shirin zuba jarin sama da dalar Amurka tiriliyan 40 kan bukatun kayayyakin more rayuwa a kasashe masu tasowa. A wancan lokacin, Biden ya ce shirin zai fi dacewa da bukatun samar da ababen more rayuwa na kasashe daban-daban fiye da shirin “ziri daya da hanya daya” da kasar Sin ta gabatar.

Amma rashin tsari da neman cimma moriya ta siyasa, wancan shirin bai je ko’ina ba, saboda nuna bangaranci a Amurka. Kuma har zuwa wannan lokaci adadin kudaden da aka saka a cikin ayyukan da ke da alaka, dalar Amurka miliyan 6 ne kawai, karya fure take ba ’ya’ya”.

Sanin kowane cewa, kasashe masu tasowa suna fuskantar babban gibin kudade wajen gina ababen more rayuwa. Idan har da gaske ‘yan siyasar Amurka suna son ba da taimakon kudi, wannan abu ne mai kyau.

Amma idan har ba sa son baiwa kasashe masu tasowa gudummawa, sai neman su yi wasa da hankali ne, to duk wasu sabbin sharuddan da suka kirkira, ba za su iya yaudarar kasashen da suka amfana da fa’idar shawarar “ziri daya da hanya daya” da kasar Sin ta gabatar ba. Ruwan da ya duka ka, shi ne ruwa.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Muguwar Niyya Ba Za Su Samu Biyan Bukata Ba

Next Post

Yadda ‘Yan Filato Ke Rajistar Katin Zabe Duk Da Mamakon Ruwan Sama

Related

Hangzhou
Daga Birnin Sin

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

10 hours ago
Syria
Daga Birnin Sin

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

11 hours ago
Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

12 hours ago
Amurka
Daga Birnin Sin

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

14 hours ago
’Yan Wasan Kasar Sin Sun Zarce Tsammani A Hangzhou 
Daga Birnin Sin

’Yan Wasan Kasar Sin Sun Zarce Tsammani A Hangzhou 

1 day ago
Za A Wallafa Sharhin Xi Kan Ciyar Da Zamanantar Da Kasar Sin Gaba
Daga Birnin Sin

Za A Wallafa Sharhin Xi Kan Ciyar Da Zamanantar Da Kasar Sin Gaba

1 day ago
Next Post
Yadda ‘Yan Filato Ke Rajistar Katin Zabe Duk Da Mamakon Ruwan Sama

Yadda 'Yan Filato Ke Rajistar Katin Zabe Duk Da Mamakon Ruwan Sama

LABARAI MASU NASABA

Mata

Ilimin ‘Ya’ya Mata: Kano Ta Fara Bai Wa ‘Yan Mata 45,000 Tallafin N20, 000

October 2, 2023
Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

October 1, 2023
Tinubu

Ranar ‘Yanci: Tinubu Ya Kara Wa Kananan Ma’aikata N25,000 Kan Albashinsu

October 1, 2023
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

October 1, 2023
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

October 1, 2023
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

October 1, 2023
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

October 1, 2023
Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

October 1, 2023
Amurka

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

October 1, 2023
Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kafa Sashi Na Musamman A NPA Don Inganta Ayyukanta

October 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.