ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Abin Da Zai Bata Sunan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

by CMG Hausa
4 years ago

A duk lokacin da aka bullo da wata manufa ko hadin gwiwa da nufin inganta rayuwar al’ummomin kasashen duniya, ya kamata kowa ya ga sakamakon hakan a zahiri, kamar yadda shawarar “ziri daya da hanya daya” ta samarwa kasashen da ke cikinta da ma hadin gwiwar kasashen Sin da Afirka da ya haifar da gagarumin sakamakon, sabanin yadda Amurka da kawayenta ke neman bata sunan shawarar yayin taron G7 na baya-bayan da suka gudanar a kasar Jamus.

Sai dai duk wani surutu da Amurka da masu neman bata sunan shawarar za su yi, hakarsu ba za ta cimma ruwa ba, domin kan Mage ya riga ya waye, galibin kasashen da suka amfana da shawarar, ba za su taba yarda a yi musu sakiyar da babu ruwa ba.

Har kullum kasar Sin wadda ta gabatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, tana maraba da duk wata shawarar da za ta inganta muhimman ababen more rayuwar al’ummar duniya. A hannu guda kuma, tana nuna adawa ga duk wani yunkuri na bata sunan shawarar “ziri daya da hanya daya”, bisa hujjar inganta muhimman ababen more rayuwar al’umma, don cimma wani muradun siyasa.

ADVERTISEMENT

Wannan batu na zuwa ne, yayin da shugaban Amurka Joe Bide a wajen taron kolin kasashen G7, ya sanar da kaddamar da wai, wani shirin hadin gwiwa kan inganta muhimman ababen more rayuwar al’umma da zuba jari a duniya”, har ma wasu manyan jami’an gwamnatin Amurka da ba’a san ko su waye ba, sun rika furta kalamai na shafawa shawarar “ziri daya da hanya daya” ta kasar Sin bakin fenti. Duniya ta sha jin surutu da alkawura daga bangaren Amurka ba tare da cikawa ba.

Wani abin takaici ma shi ne, wai kasar da ba ta wadatu da ababen more rayuwa a cikin gidan ta ba , ita ce za ta jagoranci aiwatar da abin da ake kira ayyukan samar da ababen more rayuwa a duniya. Amma idan mutum ya ce, zai ba ka riga to ka kalli ta wuyansa.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Idan ba a manta ba, a yayin taron G7 da aka gudanar a shekarar da ta gabata, an bijiro da maganar shawarar hadin gwiwa da ake kira “Sake gina duniya mai kyau” (B3W), tare da shirin zuba jarin sama da dalar Amurka tiriliyan 40 kan bukatun kayayyakin more rayuwa a kasashe masu tasowa. A wancan lokacin, Biden ya ce shirin zai fi dacewa da bukatun samar da ababen more rayuwa na kasashe daban-daban fiye da shirin “ziri daya da hanya daya” da kasar Sin ta gabatar.

Amma rashin tsari da neman cimma moriya ta siyasa, wancan shirin bai je ko’ina ba, saboda nuna bangaranci a Amurka. Kuma har zuwa wannan lokaci adadin kudaden da aka saka a cikin ayyukan da ke da alaka, dalar Amurka miliyan 6 ne kawai, karya fure take ba ’ya’ya”.

Sanin kowane cewa, kasashe masu tasowa suna fuskantar babban gibin kudade wajen gina ababen more rayuwa. Idan har da gaske ‘yan siyasar Amurka suna son ba da taimakon kudi, wannan abu ne mai kyau.

Amma idan har ba sa son baiwa kasashe masu tasowa gudummawa, sai neman su yi wasa da hankali ne, to duk wasu sabbin sharuddan da suka kirkira, ba za su iya yaudarar kasashen da suka amfana da fa’idar shawarar “ziri daya da hanya daya” da kasar Sin ta gabatar ba. Ruwan da ya duka ka, shi ne ruwa.

CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Yadda ‘Yan Filato Ke Rajistar Katin Zabe Duk Da Mamakon Ruwan Sama

Yadda 'Yan Filato Ke Rajistar Katin Zabe Duk Da Mamakon Ruwan Sama

LABARAI MASU NASABA

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.