• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

by Abubakar Abba
2 months ago
Mai

Masu Ruwa da tsaki a fannin Man Fetur da Iskar Gas, sun jaddada bukatar kara samar da yin gasa a bangaren Man Fetur da kuma Iskar Gas da ake hakowa a Teku, mussaman domin a kara janyo masu zuba hannun jari a fannin.

Sun yi wannan kiran ne a taron tattaunawa, da kungiyarsu da ake kira a turance ta Edtractibe360 ta hadawa manema labarai a Babban Birnin Tarayyar Abuja.

  • Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela
  • Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Sun zayyano mahimmancin da ke na yin gasa a fannin, mussaman domin a tabbatar da an tsaftacen bangaren da kuma samar masa, da rasuwar da ta dace.

Daya daga cikin masu ruwa da tsaki a fannin Ademola Adigun, ya jaddada cewa, fannin na hako Man daga Taku, ba wai ana nufin a dakatar da shigo Man daga kasar waje bane duk da ci gaban da aka samu na kafa Matatar Mai ta Dangote a kasar nan.

Ademola ya kara da cewa, kafa Matatar Man ta Dangote, wata babbar nasarar ce ga kasar nan wajen zuba hannun jari wacce kuma ta zamo abin tunkaho ga kasar, amma tana fuskantar rashin samun gasa ta kasuwa na karfin iya tace yawan Man da ake bukata a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

“Dole ne fannin na hako Man daga Taku, ya zamo an samar da gudanar da gasa kuma dole a tabbatar da an yi adalci da bin ka’ida domin masu amfani da Man, su amfana,” A cewar Adigun.

“Samun Matatar Man ta Dangote, wata babbar nasara ce, ta zuba hannun jari a fannin Mai na kasar nan,.” A cewarsa.

“A shekaru baya, Nijeriya ta fi yin dogaro wajen shigo da Man Fetur zuwa cikin kasar, amma bisa samun kafa Matatar Man ta Dangote, labarin ya sauya, kan shigo da Man da sauran dangoginsa zuwa cikin kasar nan daga wasu kasashen waje,” Inji Adigun.

Ya kara da cewa, amma duk da zuba hannun jari a fannin na hako Man daga Taku, har yanzu Fannin na ci gaba da fuskantar karancin samun gasa wajen sarrafa Man da kuma na dangoginsa.

“Nijeriya za ta ci gaba da shigo da Man daga kasar waje amma ba wai domin kasar ta rasa samun kasuwanni bane sai dai kawai saboda rashin samun wani zabin da ya kamata” A cewarsa.

Shi ma a na sa jawabin a wajen ttaron kwararren a bangaren shari’a Olasubomi Chuku, ya zayyano wasu daga cikin matakan na gasar wanda ya danganta a matasyin babbar gasa dake tattare da fannin.

Shugabar ta kungiyar Juliet Ukanwosu ta sanar da cewa, tun lokacin da Gwamnatin Tarayya ta cire tallafin Man Fetur hakan ya sanya an samu daidaito farashin Man Fetur a gidajen sayar da Man da ke a kasar.

A cewarta, hakan ya kara haifar da zazzafar gasa a tsakanin masu hada-hadar kasuwanci na Man a kasar.

“Wannan ya kara sanyawa an samu sauye- sauye a farashin na Man Fetur da haifar wa kasuwanci wani sabon juyi wanda hakan ya kuma shafi masu amfani da Man a yau da kullum, ” Inji Juliet.

Kazalika, Shugabar ta lissafo wasu daga cikin kalubalen da suka hada da, tsadar kudaden aiki da yawan samun hauhawan farashin kudaden musaya na ketare da dogaro kan Man Fetur da ake shigowa da shi cikin kasar nan da kalubalen shigo da kayan aikin da sauransu. wanda hakan ke kara jefa fannin s cikin wani kalubalen.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

October 25, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
Tattalin Arziki

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Next Post
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.