• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

by Abubakar Abba
3 hours ago
in Tattalin Arziki
0
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu Ruwa da tsaki a fannin Man Fetur da Iskar Gas, sun jaddada bukatar kara samar da yin gasa a bangaren Man Fetur da kuma Iskar Gas da ake hakowa a Teku, mussaman domin a kara janyo masu zuba hannun jari a fannin.

Sun yi wannan kiran ne a taron tattaunawa, da kungiyarsu da ake kira a turance ta Edtractibe360 ta hadawa manema labarai a Babban Birnin Tarayyar Abuja.

  • Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela
  • Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Sun zayyano mahimmancin da ke na yin gasa a fannin, mussaman domin a tabbatar da an tsaftacen bangaren da kuma samar masa, da rasuwar da ta dace.

Daya daga cikin masu ruwa da tsaki a fannin Ademola Adigun, ya jaddada cewa, fannin na hako Man daga Taku, ba wai ana nufin a dakatar da shigo Man daga kasar waje bane duk da ci gaban da aka samu na kafa Matatar Mai ta Dangote a kasar nan.

Ademola ya kara da cewa, kafa Matatar Man ta Dangote, wata babbar nasarar ce ga kasar nan wajen zuba hannun jari wacce kuma ta zamo abin tunkaho ga kasar, amma tana fuskantar rashin samun gasa ta kasuwa na karfin iya tace yawan Man da ake bukata a kasar.

Labarai Masu Nasaba

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

“Dole ne fannin na hako Man daga Taku, ya zamo an samar da gudanar da gasa kuma dole a tabbatar da an yi adalci da bin ka’ida domin masu amfani da Man, su amfana,” A cewar Adigun.

“Samun Matatar Man ta Dangote, wata babbar nasara ce, ta zuba hannun jari a fannin Mai na kasar nan,.” A cewarsa.

“A shekaru baya, Nijeriya ta fi yin dogaro wajen shigo da Man Fetur zuwa cikin kasar, amma bisa samun kafa Matatar Man ta Dangote, labarin ya sauya, kan shigo da Man da sauran dangoginsa zuwa cikin kasar nan daga wasu kasashen waje,” Inji Adigun.

Ya kara da cewa, amma duk da zuba hannun jari a fannin na hako Man daga Taku, har yanzu Fannin na ci gaba da fuskantar karancin samun gasa wajen sarrafa Man da kuma na dangoginsa.

“Nijeriya za ta ci gaba da shigo da Man daga kasar waje amma ba wai domin kasar ta rasa samun kasuwanni bane sai dai kawai saboda rashin samun wani zabin da ya kamata” A cewarsa.

Shi ma a na sa jawabin a wajen ttaron kwararren a bangaren shari’a Olasubomi Chuku, ya zayyano wasu daga cikin matakan na gasar wanda ya danganta a matasyin babbar gasa dake tattare da fannin.

Shugabar ta kungiyar Juliet Ukanwosu ta sanar da cewa, tun lokacin da Gwamnatin Tarayya ta cire tallafin Man Fetur hakan ya sanya an samu daidaito farashin Man Fetur a gidajen sayar da Man da ke a kasar.

A cewarta, hakan ya kara haifar da zazzafar gasa a tsakanin masu hada-hadar kasuwanci na Man a kasar.

“Wannan ya kara sanyawa an samu sauye- sauye a farashin na Man Fetur da haifar wa kasuwanci wani sabon juyi wanda hakan ya kuma shafi masu amfani da Man a yau da kullum, ” Inji Juliet.

Kazalika, Shugabar ta lissafo wasu daga cikin kalubalen da suka hada da, tsadar kudaden aiki da yawan samun hauhawan farashin kudaden musaya na ketare da dogaro kan Man Fetur da ake shigowa da shi cikin kasar nan da kalubalen shigo da kayan aikin da sauransu. wanda hakan ke kara jefa fannin s cikin wani kalubalen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Mai
ShareTweetSendShare
Previous Post

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Next Post

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

Related

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

2 hours ago
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

4 hours ago
Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

1 week ago
NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta
Tattalin Arziki

NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

1 week ago
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
Tattalin Arziki

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji
Tattalin Arziki

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

3 weeks ago
Next Post
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.