• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Sarrafa Waken Soya Na Neman A Haramta Fitar Da Shi Waje

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Masu Sarrafa Waken Soya Na Neman A Haramta Fitar Da Shi Waje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar masu sarrafa mai daga waken soya zuwa man girke-girke ta kasa (OSPAN), ta bayyana jarinta na dala miliyan 250 da ta zuba; don sarrafa mai daga Irin Waken Soya, a matsayin wanda ke fuskantar barazana, sakamakon yadda ake fitar da Waken Soyar zuwa kasashen waje.

Wannan korafin na kunshe ne a cikin sanarwar da Shugaban Kungiyar na Kasa, Sama’ila Barau Maigoro da Mataimakinsa, Mista  Hule Idyerkas suka sanya wa hannu tare da fitar da shi a Garin Lafiya da ke a Jihar Nasarawa.

  • Hizba Ta Gana Da Kungiyar Masu Bege, Ta Bukaci Su Tsabtace Harshe
  • Na Fi Jin Dadin Rubutu Da Sassafe Ko Dare – Princess Mazadu

Sanarwar ta yi kira da a haramta fitar da Waken Soya daga Nijeriya zuwa sauran kasashen ketare, domin a karfafa wadanda suke sarrafa Irin Waken Soyar zuwa man girki; kwarin guiwa.

A cewar sanarwar, idan aka sarrafa man daga Irin na Waken Soya zuwa man girki, hakan zai bayar da dama wajen sarrafa  ainahin danyen man Waken Soyar da za a rika yin amfani da shi a cikin kasar nan, wanda hakan zai taimaka wajen karya farashin sauran man girki a Nijeriya.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, akwai ‘ya’yan kungiyar manya da matsakaita da suka zuba jarinsu, domin sarrafa mai daga Irin Waken Soya zuwa man girki.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

Ta kara da cewa, a yanzu haka man girkin da ake sarrafawa daga Irin Waken Soya a kowace shekara; ya kai tan miliyan uku, inda kuma jarin da aka zuba a fannin ya kai na kimanin dala miliyan 250.

A cewar sanarwar, a yanzu haka mune a kan gaba wajen samar da aikin yi a bangaren aikin noma na fadin kasar nan, domin muna samar da ayyuka na kai tsaye sama da 200,000.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, muna so Shugaban Kasa Bola Ahmed  Tinubu da Ministan Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Dakta Doris Uzoka-Anite su sani cewa, akasarin masana’antun da ke sarrafa mai daga Irin Waken Soya zuwa man girke-girke a kasar nan, na ci gaba da kullewa sakamakon karancin kayan aiki, musamman Waken Soya.

Bugu da kari sanarwar ta bayyana cewa, Manoman Waken Soya a shekarar 2022; sun noma Waken Soya kimanin tan 680,000, amma maimakon su sayar da shi ga masu sarrafa shi a nan cikin gida, sai suka gwammace fitar da shi zuwa kasashen ketare; domin samun kazamar riba.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, wannan lamarin na ci gaba da zama babbar barazana ga tattalin arzikin wannan kasa tare da jawo koma baya ga kokarin da gwamnatin kasar ke yi na fadada tattalin arziki da kuma kokarin samo wadanda za su zuba hannin jari a fannin tattalin arzikin tare da samar da ayyukan yi a fannin sarrafa Irin Waken Soya zuwa man girki.

Kungiyar ta sanar da cewa, Nijeriya ba ta cikin jerin kasashen duniyar da ke a kan gaba, wajen noman Waken Soya, inda wannan sabon halin na fitar da Waken Soya zuwa ketare ke jawo wa masu sarrafa mai daga Irin Waken Soya a kasar nan babban koma baya.

Kazalika, kungiyar ta OPSAN ta bukaci Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ta kawo musu daukin gaggawa a kan matsalar fitar da wannan Wake na Soya da ake yi zuwa kasashen waje.

Sannan, kungiyar ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta haramta fitar da Waken Soyar na wucin gadi daga nan Nijeriya zuwa sauran kasashen waje, har sai an tabbatar an samar da wadatuwarsa a fadin wannan kasa baki-daya.

Har ila yau, kungiyar ta kara da cewa, idan aka haramta fitar da Waken Soyar daga wannan kasa zuwa kasashen ketaren na wucin gadi, hakan zai taimaka wajen kara fadadawa da kuma bunkasa masana’antun da ke sarrafa Irin Waken Soyar zuwa na man girki a kasar nan tare da kara bunkasa tattalin arziki da kara samar da ayyukan yi  ga ‘yan kasa baki-daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kammala Wasan  Karshen Damben Warriors  Na Wannan Shekarar A Kano

Next Post

Kula Da Tsaftar Hakori

Related

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

5 days ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

6 days ago
Sin Ta Gina Cibiyoyin Fasahar Aikin Gona Na Gwaji Guda 24 A Afirka
Noma Da Kiwo

Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’

2 weeks ago
Dalilin Nijeriya Na Kulla Yarjejeniya Da Kasar Sin Kan Noman Rake
Noma Da Kiwo

Dalilin Nijeriya Na Kulla Yarjejeniya Da Kasar Sin Kan Noman Rake

2 weeks ago
Nazari Kan Amfanin Noman Kanumfari
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Amfanin Noman Kanumfari

2 weeks ago
Cutar Da Ke Kassara Gonakin Tumatir Ta Sake Bulla A Jihar Kano
Noma Da Kiwo

Cutar Da Ke Kassara Gonakin Tumatir Ta Sake Bulla A Jihar Kano

3 weeks ago
Next Post
Kula Da Tsaftar Hakori

Kula Da Tsaftar Hakori

LABARAI MASU NASABA

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.