• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Sayen Abinci Suna Ɓoyewa Ne Silar Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Yunwa – Babban Manomi

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ko kadan babu hannun manoma kan hauhawar farashin kayan abinci da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da kokawa a kansa, wasu ‘yan kasuwa masu sayen amfanin gonar ne daga wurin manoma suke saya suna boyewa don sayarwa su samu kazamar riba, don haka su ya kamata mutane su zarga.

Wannan furucin ya fito ne daga bakin fitaccen manomin Masara a Arewacin wannan kasa, Adamu Muhammad Makarfi a wata tattaunawa da ya yi da LEADERSHIP Hausa a Jihar Kaduna.

  • NCRMIDP Ta Raba Wa ‘Yan Gudun Hijira 700 Kayan Abinci A Katsina
  • Kabilanci Da Magudin Zabe Ke Kassara Samun Shugabanci Nagari – Jonathan

Makarfi, wanda kuma shi ne shugaban kungiyar manoman Masara don samun riba na Arewa maso yamma ya yi nuni da cewa, duk wadanda ke cewa manoman kasar nan ne suka haddasa hauhawar farashin kayan abinci, ba su yi musu adalci ba.

Shugaban ya ci gaba da cewa, duk da cewa manomi na da burin ganin ya samu riba bayan ya yi girbi, amma kuma ba shi da burin ganin ya tsauwala wa jama’a; musaman talakawa.

Har ila yau, Makarfin ya danganta hauhawar farashin da ake ci gaba da samu na kayan abincin a kan wasu ‘yan kasuwa da ke sayen amfanin gonar manoma, musamman kanana suna boyewa; domin sayar wa da jama’a kan farashin mai yawan gaske.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Hak zalika, ya bai wa gwamnatin tarayya shawara kan tabbatar da samar da tsarin kayyade farashin kayan abinci a fadin wannan kasa baki-daya, a cewar tasa ta haka ne kawai za a iya magance yadda ake ci gaba da samun tashin farashin kayan na abinci a daukacin fadin kasar nan.

Kazalika, shugaban ya kuma bayyana cewa; ya kamata gwamnatin tarayya ta fito da wani tsari na musamman domin dakile wasu ‘yan kasuwa masu zuwa wurin manoma, musamman kanana suna saye amfanin gonarsu cikin rahusa, domin boyewa su sayarwa da al’umma da tsada.

Har wa yau, da yake yin bayani a kan shirye-shiryen noman bana, Makarfiya bayyana cewa; akasarin manoma a kasar nan, musamman kanana ba za su iya yin noma a bana ba.

Ya kara da cewa, bayanai sun nuna cewa; musaman matsalar tsadar takin zamani a bana kusan ya fi na bara, sannan kusan a bana farashin buhun taki duk guda daya a wurin ‘yan kasuwa ya kai kimanin Naira dubu 40 zuwa sama, ya danganta da irin nau’in takin.

A cewar tasa, a kakar noman bara kusan an sayar da takin ne a kan Naira 30,000.
Bugu da kari, shugaban ya sanar da cewa; wata matsalar ita ce ta tsadar magungunan feshin kwari ko na kashe ciyawa da kuma kalubalen biyan kudin ‘yan kwadago da sauransu.

Ya ci gaba da cewa, a matsayinsu na manoma bukatarsu ba wai kawai a sayar da amfanin gona da tsada a wannan kasa ba ne, amma duk da haka, ba za su so a ce manoma sun yi asara ba, domin asarar manoma; asara ce ga kasa baki-daya.

Sannan ya yi nuni da cewa, duk inda aka ce manomi ya yi noma kuma ya fadi, babban abin da ake jin tsaro, musamman ma ga manyan manoma wadanda yawancin su suke yin noman, domin su samu riba; da zarar an ce sun fadi an samu matsala; don kuwa akasarinsu suna ciwo bashi ne daga bankuna, domin yin noma da kuma kudin ruwan da ake dora musu, saboda haka asarar za ta yi musu yawa.

Adamu ya ci gaba da cewa, idan manyan manoma ba su yi noma a kasar nan ba, ko shakka babu za a samu karancin abinci, wannan dalili ne ya sa ake yin kiraye-kiraye, don zuwa kasashen ketare a sayo abincin, sannan idan aka sayo abincin daga ketare, Nijeriya za ta iya yin asara mai yawan gaske, domin hakan zai iya durkusar da tattalin arzikinta.

Haka zalika, ya yi nuni da cewa, idan misali aka je aka sayo tan miliyan biyu na Masara don shigo da shi Nijeriya, sai an kashe akalla kusan Naira tiriliyan daya, sannan ban da sauran amfanin gona; kasar nan na bukatar akalla tan miliyan ashirin.

Ya ce, in har za a sayo Masara a kasar waje ba a noma cikin gida ba, akalla za mu yi asarar zunzurutun kudi kimanin Naira tirilyan goma, saboda haka; idan ba a bai wa manoman wannan kasa taimakon da ya dace ba, ba karamar matsala ce za ta afku ba.

Sannan, ya yi kira na musamman ga gwamnatin tarayya da ta jihohi da kuma kananan hukumomi, su mayar da hankali wajen bunkasa noman rani, domin kuwa a cewar tasa ya zama wajibi a samar da kyakkyawan tsari, amma idan ba a yi hakan ba; ba mu san irin abin da zai faru a wannan kasa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Daliban Tsangaya 15 A Sakkwato

Next Post

Sojojin Nijeriya Sun Yi Nasarar Fatattakar ‘Yan Ta’adda A Katsina

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

1 week ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

4 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

4 weeks ago
Next Post
Sojoji

Sojojin Nijeriya Sun Yi Nasarar Fatattakar ‘Yan Ta’adda A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.