ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Nijeriya Sun Yi Nasarar Fatattakar ‘Yan Ta’adda A Katsina

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Sojoji

Sojojin Nijeriya sun kai farmaki a hanyar Maikusa da ya kai su ga samun nasarar kashe babban kwamandan ‘yan ta’addan da Modi Modi ke jagoranta a Jihar Katsina. Wannan farmakin da aka aiwatar a Kananan Hukumomin Kurfi da Safana, ya nuna irin jajircewar da sojoji ke yi na kawar da ta’addanci a yankin.

A yayin wannan kazamar arangamar, sojojin sun fuskanci turjiya daga ‘yan bidigar amma duk haka, sun nuna bajinta, inda suka yi galaba akan su da karfi ta hanyar sakin wuta babu sassautawa.

  • Mahara Sun Sace Dalibai 200 A Kauyen Kaduna
  • Hukumomin Sauraron Korafe-Korafen Jama’a Na Kasar Sin Sun Lashi Takobin Samar Da Muhallin Kasuwanci Mai Kiyaye Doka

Sakamakon wannan nasara da aka samu ya kai ga kashe Maikusa da wasu ’yan ta’adda uku, wanda hakan ya nuna muhimmin ci gaba da ake samu na yunkurin kakkabe sansanonin ‘yan ta’addan.

ADVERTISEMENT

A ci gaba da musayar wutar, sojojin sun kwato manyan makamai da suka hada da bindigu kirar AK-47 guda biyu, da kwanson harsashi, da harsashin 65 mm 7.62 mm, bindigar kirar a gida, da kakin soji mai rod-rodi. Wannan gagarumin aiki na nuni da irin tasirin da sojoji ke da shi wajen wargaza hanyoyin sadarwar ta’addanci.

Yunkurin da sojojin suka yi na kawar da ‘yan ta’addar ya kara bayyana ne yayin da sojoji suka kara fadada ayyukansu, inda suka lalata sansanonin ‘yan ta’addan a kauyukan Wurma, Shaiskawa, Yauni, Dogon Marke (Larmar Kurfi), da kuma kauyukan Ummadau da Zakka (Karamar Hukumar Safana).

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

Wannan cikakken tsari na nufin kawar da ragowar gungun ‘yan ta’adda, tare da tabbatar da dorewar tsaro da tsaro a yankin.

Rundunar sojin Nijeriya na ci gaba da kai farmaki a yankin gaba daya, inda ta nuna aniyar ta na kare yankin da kuma kawar da duk wata barazana. Wannan gagarumar nasarar na nuna jajircewar da sojoji ke yi wajen yaki da ta’addanci, wanda ke nuna wani gagarumin ci gaba na samun dauwamammen zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jihar Katsina.

Sojojin Nijeriya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
Kasar sin

Kudin Tsaro Da Kasar Sin Ke Kashewa A Bayyane Yake, Bisa Gaskiya, Mai Ma’ana Kuma Matsakaici

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.