• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Su Rike Mutuncinsu Duk Inda Suke, Allah Zai Kawo Musu Mafita – Fatima

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
in Adon Gari
0
Mata Su Rike Mutuncinsu Duk Inda Suke, Allah Zai Kawo Musu Mafita – Fatima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

FATIMA ABDULLAHI haifaffiyar Hadejia, kuma yar kasuwa mai neman na kanta, ta tattauna da shafin Adon Gari inda ta yi bayanin yadda ta tsinci kanta a matsayin ‘yar kasuwa mai zaman kanta, nasarorin da ta samu ta da kuma irin kalubalen da ta fuskanta wajen kafa sana’arta da kuma yadda take sarrafa ta, inda a ciki ta shawarci mata kan lallai su tsare mutuncinsu a duk inda suke, domin idan sun yi haka Allah zai kawo musu mafita, ga dai yadda tattaunawar tasu ta kasance tare da BILKISU TIJJANI KASSIM:

Da fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki

Fatima Abdullahi Muhammad. Iyaye na haifaffun Jihar jigawa ne cikin Karamar Hukumar Hadejia. Na girma a Garin Kano na yi makaranta a Kano kuma ni ce ta farko a wajen mamana da babana. Wannan ne takaitaccen tarihina.

Shin ke matar aure ce?

A’a ba ni da aure, muna dai niyya in sha Allahu.

Labarai Masu Nasaba

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

An kusa auran kena?

Eh to kin san da yake aure mukaddari ne daga Ubangiji, sai ki ga wani idan ya zo babu bata lokaci an yi shi duk zaman da ka yi sai ki ga ya wuce an manta da shi. Yanzu dai gaskiya takamaimai babu maganar aure muna sa ran Allah ya kawo mana miji nagari.

Malama ‘yar kasuwa ce ko kuma ma’aikaciya?

Eh ni ‘yar kasuwa ce

Wanne irin kasuwanci kike yi?

Ina saida abubuwa da dama

Me ya ja hankalinki har kika shiga wannan kasuwanci?

Eh to a gaskiya ni tun ina karama ina ganin ana kasuwanci kuma tun lokacin yake matukar burgeni har na girma ina sha’awar kasuwancu kuma yana matukar birge ni, ni dai ina sha’awar na zama mai saye da sayarwa.

Mene ne matakin karatunki?

Matakin karatu na shi ne N.C.E. daga nan na tsaye ban ci gaba ba.

To amma kina sha’awar ciga da karatunki ne ko kuma kasuwancin kikasa a gaba?

Gaskiya ina da ra’ayin ci gaba da karatu kuma in sha Allahu ina sa ran hakan.

Wanne irin kalubale kika taba fuskanta a cikin sana’arki?

A gaskiya kin san ko wace sana’a ba ta rasa kalubale sai dai mu ce Alhamdu lillah. Babban kalubale na shi ne bai wuci maganar bashi ba mutane su dauki kaya ba sa son biyan kudi wani idan kai wa miutum magana ya nemi ya gaya maka maganar banza kai da kayanka aka dauka, wani kuma ma ba zai bayar ba sai ka zo ka yi ta rigima har ka bar shi wasu kuma ba sa son daukar kayan idan ba su da kudi wadanda ke tsoron Allah kenan, wani kuma idan ya dauka daga ya samu zai bayar, to kin gani ba za a taba kasuwanci a ce babu bashi ba sai dai ka san wanda za ka ba wa. Allah ya bamu kasuwa mai albarka.

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika samu?

Alhamdu lillah mun samu na sarori da dama ana ta samun ci gaba, kasuwanci yana ta bunkasa sosai ma, Allah mun gode maka.

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da sana’arki?

Ina matukar jin dadi wajen biya ma kaina bukatu ba tare da na tambaya a yi min ba wannan gaskiya yana faranta min rai sosai har ma ina taimaka wa wasu Alhamdu lillah.

Ta wacce hanya kike bi wajen tallata sana’arki?

Kafar sada dumunta, kamar WhatsApp, Face book, insgram, da dai sauransu.

Dame kike so mutane su rika tunawa da ke?

Kyawawan halayya da kuma kokarin cika alkawari na, da kuma idan mutum ya sayi kayana hankalina ba ya kwanciya har sai kayan ya shiga hannunsa ya tabbatar min da abin da ya saya ya samu.

Wanne irin addu’a ne idan aka yi miki kike jin dadu?

A ce min Allah ya jikan mahaifiyata a gaskiya duk wanda ya ce min Allah ya jikan mahaifiyata ba karamin jin dadi nake ba kuma wanda ya fada min yana shiga raina.

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Sun bani goyan baya dari bisa dari.

Kawaye fa?

Su ma suna ba ni hadin kai sosai suna kuma taya ni tallata kayana na gode musu.

Me kika fiso cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Cikin kayan sawa na fi son abaya ko atamfa, kayan kwalliya kuma gaskiya ni abociyar kwalliya ce ina son kowanne in dai zan yi amfani da shi ya yi min kyau to gaskiya ina son shi.

A karshe wace irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

Su dage da neman na kansu.kum su rike mutuncin su a duk inda suke. Sannan kuma su rike gaskiya da amana a kowane hali mutum ya tsinci kanshi Allah zai kawo mafita.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Lalata Haramtattun Rijyoyin Mai 7 Da Jiragen Ruwa 4 A Ribas

Next Post

Burina Na Yi Rubutun Da Ko Ba Ni A Yi Alfahari Da Shi Ba Na Allah Wadai Ba – Mustapha

Related

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

5 days ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

3 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

3 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

5 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

5 months ago
Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad
Adon Gari

Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad

6 months ago
Next Post
Burina Na Yi Rubutun Da Ko Ba Ni A Yi Alfahari Da Shi Ba Na Allah Wadai Ba – Mustapha

Burina Na Yi Rubutun Da Ko Ba Ni A Yi Alfahari Da Shi Ba Na Allah Wadai Ba - Mustapha

LABARAI MASU NASABA

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.