ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Burina Na Yi Rubutun Da Ko Ba Ni A Yi Alfahari Da Shi Ba Na Allah Wadai Ba – Mustapha

by Primcess Fatima Zarah Mazadu
2 years ago
Rubutun

Daya daga cikin marubuta littattafan Hausa na yanar gizo MUSTAPHA ABDULLAHI ABUBAKAR, ya bayyanawa masu karatu babban dalilin da ya sa ya tsunduma harkar rubutu tare da abin da ya ke son cimma game da rubutu, har ma da wasu batutuwan masu yawa wadanda suka shafi rayuwarsa. Ga dai tattaunawar tare da PRINCESS FATIMA ZARAH MAZADU Kamar haka:

Da farko za ka fara fada wa masu karatu cikakken sunanka tare da dan takaitaccen tarihinka…

Sunana Mustapha Abdullahi Abubakar, an haifi ni a Rimin Zayam da ke  karamar Hukumar toro na jihar Bauchi. Na yi karatun ‘Nursary and Primary’ a ‘L.E.A Primary School’ da ke karamar hukumar Jos ta kudu na Jihar filato wato Jos. Inda cikin yarda Allah na ci gaba da karatuna na sakandare a ‘Nurul Islam High School’ duk a garin Jos Jihar filato. Inda yanzu na samu shadar kammala karatuna na aikin jarida a kwalejin kimiya da fasaha na  ‘Abubakar Tatari Ali Polytechnic’, da ke jihar Bauchi. Inda yanzu haka na ci gaba da karatuna na HND duka a garin Bauchi.

ADVERTISEMENT

Me ya ja hankalinka har ka tsunduma harkar rubutu?

Abin da ya ja hankali na fara Rubutu shi ne yaudarar da a ka yi min lokacin ina soyayya da wata wacce ta yaudare ni shi ne dalilina na fara rubutu.

LABARAI MASU NASABA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

Rubutun

Kamar wane labari ka fi maida hankali a kai wajen rubutawa?

Labarin da na fi maida hankali shi ne labaran hikayoyi, da kuma na soyayya.

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?

Gaskiya ne na yi gwagwarmaya sosai, duba da lokacin ban ma san ta ya ya zan fara yin rubutun ba, da kuma salon rubutun da zan yi.

Za ka yi kamar shekara nawa da fara rubutu?

Na kai shekaru biyar ina rubutu.

Ka rubuta labarai sun kai kamar guda nawa?

Gaskiya na yi rubutun labari da yawa  kamar; Akwai Dalili, Tarbiya A yau, Mai Hakuri, Rayuwar Addini, Dan Baiwa, Bakar Alaka.

Wane labari ne ya zamo bakandamiyarka cikin labaran da ka rubuta?

A cikin rubutuna da na yi bakandamiyata shi ne ‘Akwai Dalili” wanda na fi so kenan, kusan dukka labarin soyayyata ne.

Wane labari ne cikin labaranka ya fi ba ka wahala wajen rubutawa, kuma me ya sa?

Wanda ya fi ba ni wahala shi ne ‘A kwai Dalili’, domin lokacin da nake rubutun littafin yana tuna min abubuwa da dama game da rayuwata, da wacce muka yi soyayya.

Wane irin nasarori ka samu game da rubutu?

Nasarorin da na samu shi ne na Hadu da manyan marubuta wanda nake kallo a TB ko jin labaransu a gidajan rediyo, kamar Alan waka, Abba Abubakar Yakubu daga Jos, Fadila H. Aliyu, da sauran marubuta da dama, sai dai na ce Ma sha Allah.

Wanne irin kalubale ka fuskanta game da rubutu?

Kamar yadda na ce na samu kalubale sosai, kama daga ‘yan’uwana da ma abokai na, amma yanzu dai Alhamdullahi.

Lokacin da ka fara sanar wa iyayenka kana son fara yin rubutu, ko a kwai wani kalubale da ka fuskanta daga gare su?

Gaskiya ban fuskanci wani kalubale daga iyayena ba, sai dai ma  fatan nasara daga bakinsu.

A gabadaya labaran da ka rubuta shin ka taba buga wani?

Ban buga littafi ko daya ba yanzu haka, amma a kwai wanda yanzu haka saura kadan ya fito kasuwa da yardar Allah.

Mene ne burinka na gaba game da rubutu?

Burina a harkar rubutu shi ne na yi rubutu wanda ko ba ni a raye a yi alfahari da shi ba wanda za a rika Allah wadai da shi ba.

Wane abu ne ya taba faruwa da kai na farin ciki ko akasin haka game da rubutu?

Na samu yabo daga wajan mutane da dama gaskiya, an taba batamin rai sau daya dalili kuwa shi ne labarin soyayyata dana rubuta.

Me ka fi yawan tunawa game da rubutu?

Na fi tunawa da cewa komai zan rubuta iyayena za su karanta, abin da nake tunawa kenan.

Ya ka dauki rubutu a wajenka?

Na dauki rubutun sana’a ce kamar ko wacce sana’a.

Bayan rubutu kana wata sana’ar ne?

Bayan rubutu, ni ma’akacin gidan Rediyo ne a garin Jos.

Ya ka ke iya hada rubutunka da aikinka?

A kwai lokacin da nake warewa na yin rubutu da kuma lokacin sana’a ta.

Kamar yaushe ka fi jin dadin yin rubutu?

Na fi yin rubutu cikin dare gaskiya, Kamar karfe 10 na dare zuwa’ 12 na dare.

Me za ka ce da makaranta labaranka?

Ina godiya sosai da irin shawarware da suke ba ni da kuma fatan Alkhari da suke yi min, Allah ubangeji ya bar zumunci.

Ko kanada wadanda za ka gaisar?

Ina gaishe da mahaifina da mahaifiyata da kuma Abba Abubakar Yakubu Dan Jarida sosai a garin Jos da duk masoya Manzon Allah (SAW).

Rubutun
Primcess Fatima Zarah Mazadu
+ postsBio
  • Primcess Fatima Zarah Mazadu
    https://hausa.leadership.ng/author/primcess-fatima-zarah-mazadu/
    Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad
  • Primcess Fatima Zarah Mazadu
    https://hausa.leadership.ng/author/primcess-fatima-zarah-mazadu/
    An Yi Min Abin Da Zuciya Da Kwakwalwa Ba Za Su Taba Mantawa Ba A Wata Kungiyar Marubuta – Maryam
  • Primcess Fatima Zarah Mazadu
    https://hausa.leadership.ng/author/primcess-fatima-zarah-mazadu/
    Na Sha Gwagwarmaya Wajen Koyon Ka’idojin Rubutu – Zarah Sunusi
  • Primcess Fatima Zarah Mazadu
    https://hausa.leadership.ng/author/primcess-fatima-zarah-mazadu/
    Ba Yadda Za A Yi Mutum Ya Yi Rubutu Ba Tare Da Allah Ya Ba Shi Baiwa Ba –Khadija

MASU ALAKA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso
Adabi

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

February 6, 2026
CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki
Adabi

CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki

January 30, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Musayar Sakon Taya Murna Da Shugaban Rikon Kwarya Na Gabon Game Da Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Jakadanci Tsakanin Sassan Biyu

Xi Jinping Ya Yi Musayar Sakon Taya Murna Da Shugaban Rikon Kwarya Na Gabon Game Da Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Jakadanci Tsakanin Sassan Biyu

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.