• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Burina Na Yi Rubutun Da Ko Ba Ni A Yi Alfahari Da Shi Ba Na Allah Wadai Ba – Mustapha

by Primcess Fatima Zarah Mazadu
1 year ago
in Adabi
0
Burina Na Yi Rubutun Da Ko Ba Ni A Yi Alfahari Da Shi Ba Na Allah Wadai Ba – Mustapha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daya daga cikin marubuta littattafan Hausa na yanar gizo MUSTAPHA ABDULLAHI ABUBAKAR, ya bayyanawa masu karatu babban dalilin da ya sa ya tsunduma harkar rubutu tare da abin da ya ke son cimma game da rubutu, har ma da wasu batutuwan masu yawa wadanda suka shafi rayuwarsa. Ga dai tattaunawar tare da PRINCESS FATIMA ZARAH MAZADU Kamar haka:

Da farko za ka fara fada wa masu karatu cikakken sunanka tare da dan takaitaccen tarihinka…

Sunana Mustapha Abdullahi Abubakar, an haifi ni a Rimin Zayam da ke  karamar Hukumar toro na jihar Bauchi. Na yi karatun ‘Nursary and Primary’ a ‘L.E.A Primary School’ da ke karamar hukumar Jos ta kudu na Jihar filato wato Jos. Inda cikin yarda Allah na ci gaba da karatuna na sakandare a ‘Nurul Islam High School’ duk a garin Jos Jihar filato. Inda yanzu na samu shadar kammala karatuna na aikin jarida a kwalejin kimiya da fasaha na  ‘Abubakar Tatari Ali Polytechnic’, da ke jihar Bauchi. Inda yanzu haka na ci gaba da karatuna na HND duka a garin Bauchi.

Me ya ja hankalinka har ka tsunduma harkar rubutu?

Abin da ya ja hankali na fara Rubutu shi ne yaudarar da a ka yi min lokacin ina soyayya da wata wacce ta yaudare ni shi ne dalilina na fara rubutu.

Labarai Masu Nasaba

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

Rubutun

Kamar wane labari ka fi maida hankali a kai wajen rubutawa?

Labarin da na fi maida hankali shi ne labaran hikayoyi, da kuma na soyayya.

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?

Gaskiya ne na yi gwagwarmaya sosai, duba da lokacin ban ma san ta ya ya zan fara yin rubutun ba, da kuma salon rubutun da zan yi.

Za ka yi kamar shekara nawa da fara rubutu?

Na kai shekaru biyar ina rubutu.

Ka rubuta labarai sun kai kamar guda nawa?

Gaskiya na yi rubutun labari da yawa  kamar; Akwai Dalili, Tarbiya A yau, Mai Hakuri, Rayuwar Addini, Dan Baiwa, Bakar Alaka.

Wane labari ne ya zamo bakandamiyarka cikin labaran da ka rubuta?

A cikin rubutuna da na yi bakandamiyata shi ne ‘Akwai Dalili” wanda na fi so kenan, kusan dukka labarin soyayyata ne.

Wane labari ne cikin labaranka ya fi ba ka wahala wajen rubutawa, kuma me ya sa?

Wanda ya fi ba ni wahala shi ne ‘A kwai Dalili’, domin lokacin da nake rubutun littafin yana tuna min abubuwa da dama game da rayuwata, da wacce muka yi soyayya.

Wane irin nasarori ka samu game da rubutu?

Nasarorin da na samu shi ne na Hadu da manyan marubuta wanda nake kallo a TB ko jin labaransu a gidajan rediyo, kamar Alan waka, Abba Abubakar Yakubu daga Jos, Fadila H. Aliyu, da sauran marubuta da dama, sai dai na ce Ma sha Allah.

Wanne irin kalubale ka fuskanta game da rubutu?

Kamar yadda na ce na samu kalubale sosai, kama daga ‘yan’uwana da ma abokai na, amma yanzu dai Alhamdullahi.

Lokacin da ka fara sanar wa iyayenka kana son fara yin rubutu, ko a kwai wani kalubale da ka fuskanta daga gare su?

Gaskiya ban fuskanci wani kalubale daga iyayena ba, sai dai ma  fatan nasara daga bakinsu.

A gabadaya labaran da ka rubuta shin ka taba buga wani?

Ban buga littafi ko daya ba yanzu haka, amma a kwai wanda yanzu haka saura kadan ya fito kasuwa da yardar Allah.

Mene ne burinka na gaba game da rubutu?

Burina a harkar rubutu shi ne na yi rubutu wanda ko ba ni a raye a yi alfahari da shi ba wanda za a rika Allah wadai da shi ba.

Wane abu ne ya taba faruwa da kai na farin ciki ko akasin haka game da rubutu?

Na samu yabo daga wajan mutane da dama gaskiya, an taba batamin rai sau daya dalili kuwa shi ne labarin soyayyata dana rubuta.

Me ka fi yawan tunawa game da rubutu?

Na fi tunawa da cewa komai zan rubuta iyayena za su karanta, abin da nake tunawa kenan.

Ya ka dauki rubutu a wajenka?

Na dauki rubutun sana’a ce kamar ko wacce sana’a.

Bayan rubutu kana wata sana’ar ne?

Bayan rubutu, ni ma’akacin gidan Rediyo ne a garin Jos.

Ya ka ke iya hada rubutunka da aikinka?

A kwai lokacin da nake warewa na yin rubutu da kuma lokacin sana’a ta.

Kamar yaushe ka fi jin dadin yin rubutu?

Na fi yin rubutu cikin dare gaskiya, Kamar karfe 10 na dare zuwa’ 12 na dare.

Me za ka ce da makaranta labaranka?

Ina godiya sosai da irin shawarware da suke ba ni da kuma fatan Alkhari da suke yi min, Allah ubangeji ya bar zumunci.

Ko kanada wadanda za ka gaisar?

Ina gaishe da mahaifina da mahaifiyata da kuma Abba Abubakar Yakubu Dan Jarida sosai a garin Jos da duk masoya Manzon Allah (SAW).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mata Su Rike Mutuncinsu Duk Inda Suke, Allah Zai Kawo Musu Mafita – Fatima

Next Post

Xi Jinping Ya Yi Musayar Sakon Taya Murna Da Shugaban Rikon Kwarya Na Gabon Game Da Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Jakadanci Tsakanin Sassan Biyu

Related

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

2 months ago
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

6 months ago
Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya
Adabi

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

7 months ago
Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk
Adabi

Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk

8 months ago
Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk
Adabi

Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk

8 months ago
Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad
Adabi

Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad

10 months ago
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Musayar Sakon Taya Murna Da Shugaban Rikon Kwarya Na Gabon Game Da Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Jakadanci Tsakanin Sassan Biyu

Xi Jinping Ya Yi Musayar Sakon Taya Murna Da Shugaban Rikon Kwarya Na Gabon Game Da Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Jakadanci Tsakanin Sassan Biyu

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.