ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Su Rike Mutuncinsu Duk Inda Suke, Allah Zai Kawo Musu Mafita – Fatima

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Allah

FATIMA ABDULLAHI haifaffiyar Hadejia, kuma yar kasuwa mai neman na kanta, ta tattauna da shafin Adon Gari inda ta yi bayanin yadda ta tsinci kanta a matsayin ‘yar kasuwa mai zaman kanta, nasarorin da ta samu ta da kuma irin kalubalen da ta fuskanta wajen kafa sana’arta da kuma yadda take sarrafa ta, inda a ciki ta shawarci mata kan lallai su tsare mutuncinsu a duk inda suke, domin idan sun yi haka Allah zai kawo musu mafita, ga dai yadda tattaunawar tasu ta kasance tare da BILKISU TIJJANI KASSIM:

Da fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki

Fatima Abdullahi Muhammad. Iyaye na haifaffun Jihar jigawa ne cikin Karamar Hukumar Hadejia. Na girma a Garin Kano na yi makaranta a Kano kuma ni ce ta farko a wajen mamana da babana. Wannan ne takaitaccen tarihina.

ADVERTISEMENT

Shin ke matar aure ce?

A’a ba ni da aure, muna dai niyya in sha Allahu.

LABARAI MASU NASABA

Sirrin Mallakar Miji 

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

An kusa auran kena?

Eh to kin san da yake aure mukaddari ne daga Ubangiji, sai ki ga wani idan ya zo babu bata lokaci an yi shi duk zaman da ka yi sai ki ga ya wuce an manta da shi. Yanzu dai gaskiya takamaimai babu maganar aure muna sa ran Allah ya kawo mana miji nagari.

Malama ‘yar kasuwa ce ko kuma ma’aikaciya?

Eh ni ‘yar kasuwa ce

Wanne irin kasuwanci kike yi?

Ina saida abubuwa da dama

Me ya ja hankalinki har kika shiga wannan kasuwanci?

Eh to a gaskiya ni tun ina karama ina ganin ana kasuwanci kuma tun lokacin yake matukar burgeni har na girma ina sha’awar kasuwancu kuma yana matukar birge ni, ni dai ina sha’awar na zama mai saye da sayarwa.

Mene ne matakin karatunki?

Matakin karatu na shi ne N.C.E. daga nan na tsaye ban ci gaba ba.

To amma kina sha’awar ciga da karatunki ne ko kuma kasuwancin kikasa a gaba?

Gaskiya ina da ra’ayin ci gaba da karatu kuma in sha Allahu ina sa ran hakan.

Wanne irin kalubale kika taba fuskanta a cikin sana’arki?

A gaskiya kin san ko wace sana’a ba ta rasa kalubale sai dai mu ce Alhamdu lillah. Babban kalubale na shi ne bai wuci maganar bashi ba mutane su dauki kaya ba sa son biyan kudi wani idan kai wa miutum magana ya nemi ya gaya maka maganar banza kai da kayanka aka dauka, wani kuma ma ba zai bayar ba sai ka zo ka yi ta rigima har ka bar shi wasu kuma ba sa son daukar kayan idan ba su da kudi wadanda ke tsoron Allah kenan, wani kuma idan ya dauka daga ya samu zai bayar, to kin gani ba za a taba kasuwanci a ce babu bashi ba sai dai ka san wanda za ka ba wa. Allah ya bamu kasuwa mai albarka.

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika samu?

Alhamdu lillah mun samu na sarori da dama ana ta samun ci gaba, kasuwanci yana ta bunkasa sosai ma, Allah mun gode maka.

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da sana’arki?

Ina matukar jin dadi wajen biya ma kaina bukatu ba tare da na tambaya a yi min ba wannan gaskiya yana faranta min rai sosai har ma ina taimaka wa wasu Alhamdu lillah.

Ta wacce hanya kike bi wajen tallata sana’arki?

Kafar sada dumunta, kamar WhatsApp, Face book, insgram, da dai sauransu.

Dame kike so mutane su rika tunawa da ke?

Kyawawan halayya da kuma kokarin cika alkawari na, da kuma idan mutum ya sayi kayana hankalina ba ya kwanciya har sai kayan ya shiga hannunsa ya tabbatar min da abin da ya saya ya samu.

Wanne irin addu’a ne idan aka yi miki kike jin dadu?

A ce min Allah ya jikan mahaifiyata a gaskiya duk wanda ya ce min Allah ya jikan mahaifiyata ba karamin jin dadi nake ba kuma wanda ya fada min yana shiga raina.

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Sun bani goyan baya dari bisa dari.

Kawaye fa?

Su ma suna ba ni hadin kai sosai suna kuma taya ni tallata kayana na gode musu.

Me kika fiso cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Cikin kayan sawa na fi son abaya ko atamfa, kayan kwalliya kuma gaskiya ni abociyar kwalliya ce ina son kowanne in dai zan yi amfani da shi ya yi min kyau to gaskiya ina son shi.

A karshe wace irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

Su dage da neman na kansu.kum su rike mutuncin su a duk inda suke. Sannan kuma su rike gaskiya da amana a kowane hali mutum ya tsinci kanshi Allah zai kawo mafita.

Allah
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?

MASU ALAKA

Sirrin Mallakar Miji 
Adon Gari

Sirrin Mallakar Miji 

January 25, 2026
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
Next Post
Burina Na Yi Rubutun Da Ko Ba Ni A Yi Alfahari Da Shi Ba Na Allah Wadai Ba – Mustapha

Burina Na Yi Rubutun Da Ko Ba Ni A Yi Alfahari Da Shi Ba Na Allah Wadai Ba - Mustapha

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.