Bisa umarnin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, Mataimakinsa Kashim Shettima zai wakilci Nijeriya a bikin rantsar da shugaban ƙasa mai jiran gado na Gabon, Brice Clotaire Oligui Nguema, a Libreville a yau.
Oligui Nguema, wanda ya taɓa rike muƙamin shugaban riƙon ƙwarya tun a watan Agusta 2023, ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na ranar 12 ga Afrilu da gagarumin rinjaye, inda ya samu kashi 94.85% na yawan ƙuri’un da aka kaɗa (ƙuri’u 58,074) kamar yadda Kotun Tsarin Mulki ta Gabon ta tabbatar.
- Shettima Ya Gayyaci Shugaban NAHCON Da Mambobin Hukumar Kan Shirye-shiryen Hajjin 2025
- Masu Sa Hotona A Soshiyal Midiya Suna Yabo Babu Abin Da Za Su Samu – Hadiza Gabon
Ya doke ‘yan takara bakwai, ciki har da tsohon Firayim Minista Alain Claude Bilie-By-Nze, wanda ya zo na biyu da kashi 3% kacal na yawan ƙuri’un.
Halartar Nijeriya tana nuna goyon bayanta ga tsarin dimokuraɗiyya da kwanciyar hankula a yankin Afrika ta tsakiya. Nijeriya ta kuma jaddada sha’awarta ta ci gaba da inganta zaman lafiya a nahiyar.
Ana sa ran Mataimakin Shugaban Ƙasa zai komo Nijeriya nan da nan bayan bikin. Taron na cikin manufofin ketare na Najeriya na kara karfin dangantaka da kasashen Afirka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp