• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mataimakin Shugaban Kasa Ya Buɗe Sabon Gidan Gwamnatin Bauchi

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Bauchi

Mataimakin Shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima a ranar Asabar ya buɗe sabon gidan Gwamnatin Jihar Bauchi da gwamnatin Gwamna Bala Muhammad ta gina domin saukaka aiki da kyautata harkokin mulki.

Da ya ke jawabi a wajen taron, Shettima ya jinjinawa irin tunanin Gwamna Bala wajen ganin ya sabunta jihar, ya kuma yi kira ga Gwamnonin Arewa maso gabas da su maida hankali wajen ganin sun gudanar da kyawawan ayyukan da za su kai ga taimaka wa shiyyar.

  • Al’adu Masu Ban Al’ajabi Da Suka Ki Bacewa Duk Da Sauyin Zamani A Afirka
  • Ana Zargin Wani Hadimin ‘Yar Majalisa Da Yi Wa Almajiri Fyade A Kaduna

Ya na mai cewa, “Tabbas Gwamnonin Arewa maso gabas su na matukar kokari wajen kyautata mulki”, sai ya kirasu da su kara azama wajen kyautata rayuwar jama’arsu.

Shettima ya taya Gwamna da al’ummar Bauchi murnar samun sabon Gidan Gwamnatin da zamanantar da shi domin saukaka aiki, ya kuma yaba wa gwamnan kan ayyukan raya birane da karkara.

Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

Tun da farko a jawabinsa, Bala Muhammad ya nuna matukar farin cikinsa a bisa amsar gayyatarsu da mataimakin Shugaban kasan ya yi, ya ce, aikin zamanantar da fadar Gwamnatin Jihar na daga cikin mafarkan da ya jima ya na yi wajen ganin ya kyautata rayuwar al’umma.

Bala Muhammad ya kuma tabbatar da cewa, zai cigaba da zage damtse wajen ganin tattalin arziki ya ci gaba da bunkasuwa a Jihar, sai ya yi kira ga masu ruwa da tsaki da al’ummar jihar da su ci gaba da bai wa gwamnatinsa da sauran Gwamnonin Arewa maso gabas goyon baya domin tabbatar da ci gaban yankin.

Bauchi

Daga cikin wadanda suka kasance a wajen kaddamar da fadar har da kungiyar Gwamnonin Arewa maso gabas; Tsohon Gwamnan Bauchi a zamanin mulkin soja, Manjo-janar Abutu Garuba; Tsoffin Gwamnonin Jihar, Alhaji Ahmed Adamu Muazu, Muhammad Abubakar, da sanatoci da ‘yan majalisu da sauran su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260
Manyan Labarai

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
gaza
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
Next Post
Gimbiyoyin Kannywood (2)

Gimbiyoyin Kannywood (2)

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.