ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gimbiyoyin Kannywood (2)

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
Kannywood

LABARAI MASU NASABA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

Nafisa Abdullahi

Kannywood

Wannan suna ba boye yake ba a arewacin Nijeriya musamman ga wadanda suke da sha’awar kallon fina-finan Hausa, tsawon shekaru 10 da suka gabata Nafisa Abdullahi na daga cikin manyan jarumai mata da tauraruwarsu ke haskawa a wannan fanni na masana’antar Kannywood.

An bayyana Nafisa a matsayin jarumar da take da matukar kwarewa a kowane irin matsayi aka bata a cikin shirin fim musamman na tausayi ko kuma akasin haka, Nafisa ta fito a manyan fina-finan Hausa na Kannywood da suka hada da Lamiraj, Ya Daga Allah da kuma Sai Wata Rana wanda shi ne shiri na farko da ya haskakata a idon Duniya har aka santa a matsayin babbar jaruma a masana’antar Kannywood.

Rahama Sadau

Kannywood

Rahama Sadau ta zama kallabi a tsakanin rawuna idan aka zo maganar shirin fim a Nijeriya, inda ta zama jaruma ta farko da ta fito a cikin masana’antun fina-finai uku da suka hada da Kannywood, Nollywood sai kuma Bollywood na kasar Indiya kuma duk a cikin wadannan Rahama ta taka muhimmiyar rawar da ba kowace irin jaruma ce za ta iya takawa ba.

Rahama Sadau na daga cikin jaruman fina-finan Hausa da suke iya magana da yare daban-daban kamar Hausa, Turanci da kuma Indiyanci, hakan ya sa jarumar ‘yar asalin jahar Kaduna bata gamu da wani cikas ba a kokarin da take yi na shiga sassan Duniya domin ci gaba da harkar fim,daga cikin fina-finan Turanci da ta fito akwai Up North, Sons Of The Caliphate da kuma POSTCARDS.

Halima Atete

Kannywood

Wata jarumar Kannywood wadda sunanta ya karade koina a masana’antar Kannywood ita ce Halima Atete, ta zama daya tamkar dubu a lokacin da take cikin ganiyarta a masana’antar Kannywood, har ta kai ga lashe kyautar gwarzuwar jarumar Kannywood ta City People Entertainment Awards a shekarar 2013 bayan fitowarta a cikin shirin Dakin Amarya da Kona Gari.

Atete ta shahara a fina-finan Kannywood a shekarun 2010 zuwa 2017 inda ta fito a fina-finai fiye da 150, bayan harkar fim Halima tana da Gidauniyar da take taimaka wa masu karamin karfi haka zalika tana daga cikin jakadan hukumar kwallon kafa ta kasar Sifen (Laliga) tare da jarumi Ali Nuhu.

Maryam Booth

Kannywood

Maryam Booth ko kuma Dijangala kamar yadda aka fi saninta na daya daga cikin jarumai mata da suka shiga harkar fim da kafar dama, duk da cewar akwai ‘yan uwanta da suke shirin fim kafin ita ta shigo harkar, Maryam ta samu tagomashi yayin shigowarta masana’antar Kannywood inda ta samu dubban masoya tun bayan da ta fito a cikin shirinta na farko mai suna Dijangala inda anan ne ta samu wannan lakanin nata.

Bayan harkar fim Maryam tana harkar kwalliya da kwalisa, hakan ya sa ta bude shagon kwalliyarta da da radawa suna MBooth Beauty Parlour ,Dijangala na daga cikin jaruman masana’antar Kannywood da aka shaidesu da mutunta al’adar Bahaushe saboda irin suturar Hausawa da take sakawa a kowane lokaci.

Kannywood
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za’a Dakatar Da Wasa A Farkon Minti 10 Na Kowane Wasa A Kasar Argentina Saboda Girmama Messi
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Ahanor Kan Fam Miliyan 40
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
Kannywood
Nishadi

Dalilan Da Suka Sa Ba Zan Iya Auren Ɗan Film Ba —Bilkisu Bishasha

August 23, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kuɓutar Da Mutane 386 Bayan Garkuwa Da Su Shekara 10 A Dajin Sambisa

Sojoji Sun Kuɓutar Da Mutane 386 Bayan Garkuwa Da Su Shekara 10 A Dajin Sambisa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.