ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gimbiyoyin Kannywood (2)

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
Kannywood

LABARAI MASU NASABA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Nafisa Abdullahi

Kannywood

Wannan suna ba boye yake ba a arewacin Nijeriya musamman ga wadanda suke da sha’awar kallon fina-finan Hausa, tsawon shekaru 10 da suka gabata Nafisa Abdullahi na daga cikin manyan jarumai mata da tauraruwarsu ke haskawa a wannan fanni na masana’antar Kannywood.

An bayyana Nafisa a matsayin jarumar da take da matukar kwarewa a kowane irin matsayi aka bata a cikin shirin fim musamman na tausayi ko kuma akasin haka, Nafisa ta fito a manyan fina-finan Hausa na Kannywood da suka hada da Lamiraj, Ya Daga Allah da kuma Sai Wata Rana wanda shi ne shiri na farko da ya haskakata a idon Duniya har aka santa a matsayin babbar jaruma a masana’antar Kannywood.

Rahama Sadau

Kannywood

Rahama Sadau ta zama kallabi a tsakanin rawuna idan aka zo maganar shirin fim a Nijeriya, inda ta zama jaruma ta farko da ta fito a cikin masana’antun fina-finai uku da suka hada da Kannywood, Nollywood sai kuma Bollywood na kasar Indiya kuma duk a cikin wadannan Rahama ta taka muhimmiyar rawar da ba kowace irin jaruma ce za ta iya takawa ba.

Rahama Sadau na daga cikin jaruman fina-finan Hausa da suke iya magana da yare daban-daban kamar Hausa, Turanci da kuma Indiyanci, hakan ya sa jarumar ‘yar asalin jahar Kaduna bata gamu da wani cikas ba a kokarin da take yi na shiga sassan Duniya domin ci gaba da harkar fim,daga cikin fina-finan Turanci da ta fito akwai Up North, Sons Of The Caliphate da kuma POSTCARDS.

Halima Atete

Kannywood

Wata jarumar Kannywood wadda sunanta ya karade koina a masana’antar Kannywood ita ce Halima Atete, ta zama daya tamkar dubu a lokacin da take cikin ganiyarta a masana’antar Kannywood, har ta kai ga lashe kyautar gwarzuwar jarumar Kannywood ta City People Entertainment Awards a shekarar 2013 bayan fitowarta a cikin shirin Dakin Amarya da Kona Gari.

Atete ta shahara a fina-finan Kannywood a shekarun 2010 zuwa 2017 inda ta fito a fina-finai fiye da 150, bayan harkar fim Halima tana da Gidauniyar da take taimaka wa masu karamin karfi haka zalika tana daga cikin jakadan hukumar kwallon kafa ta kasar Sifen (Laliga) tare da jarumi Ali Nuhu.

Maryam Booth

Kannywood

Maryam Booth ko kuma Dijangala kamar yadda aka fi saninta na daya daga cikin jarumai mata da suka shiga harkar fim da kafar dama, duk da cewar akwai ‘yan uwanta da suke shirin fim kafin ita ta shigo harkar, Maryam ta samu tagomashi yayin shigowarta masana’antar Kannywood inda ta samu dubban masoya tun bayan da ta fito a cikin shirinta na farko mai suna Dijangala inda anan ne ta samu wannan lakanin nata.

Bayan harkar fim Maryam tana harkar kwalliya da kwalisa, hakan ya sa ta bude shagon kwalliyarta da da radawa suna MBooth Beauty Parlour ,Dijangala na daga cikin jaruman masana’antar Kannywood da aka shaidesu da mutunta al’adar Bahaushe saboda irin suturar Hausawa da take sakawa a kowane lokaci.

Kannywood
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kuɓutar Da Mutane 386 Bayan Garkuwa Da Su Shekara 10 A Dajin Sambisa

Sojoji Sun Kuɓutar Da Mutane 386 Bayan Garkuwa Da Su Shekara 10 A Dajin Sambisa

LABARAI MASU NASABA

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

July 9, 2026
Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

July 9, 2026
‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

July 9, 2026
Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

July 9, 2026
Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

July 9, 2026
Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

July 9, 2026
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

July 9, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

July 9, 2026
An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

July 9, 2026
kebbi

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.