• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mataimakiyar Sakatare Janar Ta MDD Ta Kammala Ziyarar Aikin Kwanaki 2 A Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
9 months ago
MDD

A ranar 13 ga Janairun 2025 a Abuja, Mataimakiyar Sakatare-Janar ta Majalisar Dinkin Duniya, Hajiya Amina J. Mohammed ta kammala ziyarar aiki ta kwanaki 2 a Nijeriya.

Yayin da take Nijeriya, ta yi tarurruka da dama, ciki har da ganawa da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu; Ministan Kudi kuma Ministan Tattalin Arziki, Wale Edun; Ministan Ba da Agaji, yaki da annoba da Ci gaban Jama’a, Farfesa Nentawe Goshwe Yilwatda; manyan jami’an gwamnati; Shugaban kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), Dr. Omar Alieu Touray; da kuma tawagar Majalisar Dinkin Duniya a karkashin jagorancin mai kula da ayyuka.

  • JAMB Ta Musanta Zargin Kashe Naira Biliyan 9 Wajen Ciyarwa Da Walwala 
  • Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Murar Tsuntsaye A Kano

Hajiya Amina, tare da Wakilin Babban Sakatare na Afirka ta Yamma da Sahel (UNOWAS), Leonardo Simão, a ranar 9 da 10 ga Janairu, 2025, ya shiga tare da tattara tallafi don hadin kai, kwanciyar hankali da ci gaba, karfafa hadin gwiwar dan’Adam, dorewar zaman lafiya, hadin gwiwa don aiwatar da aikin gaggawa na magance sauyin yanayi da tasirinsa, tabbatar da wadatar abinci, mafita mai dorewa ga masu hijira, da kuma yin amfani da yarjejeniyar ciniki cikin ‘yanci ta Afirka (AfCFTA) don inganta kasuwanci da tattalin arzikin Nijeriya a fadin yankin.

“Ƙasashe membobi, ciki har da Nijeriya, tare da goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya da sauran masu ruwa da tsaki, suna bukatar ba da gudummawar da aka kaddara ta kasa (NDCs) don tabbatar da mafi aminci da rayuwa mai kyau ga duniya da mutane a ko’ina,” a cewarta.

 

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

MDD

Dangane da yarjejeniyar a matsayin sakamakon taron qoli na nan gaba da aka gudanar a watan Satumbar 2024 a birnin New York, Mohammed ya jaddada cewa yarjejeniyar ta kasance tabbatacciya ta hanyar dawo da muradun ci gaba mai dorewa (SDGs).

“Yarjejeniyar ba wata ajanda ce ta daban ba daga SDGs. Daya ce, shi ya sa babin farko ya kasance kan muradun ci gaba mai dorewa (SDGs) da kuma ba da kudaden ci gaba, ya shafi zaman lafiya da tsaro na duniya; kimiyya, da fasaha da hadin gwiwar dijital; matasa da na gaba; da kuma sauya tsarin mulkin duniya,” kamar yadda ta yi bayani.

Hajiya Amina ta tabbatar da cewa MDD a Nijeriya za ta karfafa hadin gwiwarta da gwamnati ta hanyar yin aiki tukuru wajen aiwatar da tsarin hadin gwiwar Majalisar Dinkin Duniya da Nijeriya (2023 zuwa 2027), kuma za ta ci gaba da bayar da goyon baya ga ci gaban al’ummar Nijeriya, ba tare da barin kowa a baya ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Labarai

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
Next Post
Abubuwan Dake Kunshe Cikin Rahoton Shekara-Shekara Game Da Cinikin Shige Da Fice Na Kasar Sin

Abubuwan Dake Kunshe Cikin Rahoton Shekara-Shekara Game Da Cinikin Shige Da Fice Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.