• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakan Sin Na Yaki Da COVID-19 Sun Haifar Da Da Mai Ido

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Matakan Sin Na Yaki Da COVID-19 Sun Haifar Da Da Mai Ido
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cibiyar yada shirye-shirye da harsunan Asiya da Afrika, na Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG, ya gudanar da wani taron karawa juna sani kan yanayin kasar Sin a kokarinta na dakile cutar COVID-19.

Idan ba a manta ba, kasar Sin ce kasa ta farko da ta sanar da bullar cutar a hukumance ga hukumar lafiya ta duniya a karshen shekarar 2019, duk da cewa, sakamakon tarin bincike sun nuna cewa, an samu bullar cutar a wurare da dama kafin a same ta a kasar Sin. Baya ga haka, har kawo yanzu, babu wata kasa da ta taka rawar gani wajen yaki da cutar kamar kasar ta Sin.

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da “Bikin Nuna Al’adun Larabawa”

Wasu kafafen yada labarai na yammacin duniya da ma gwamnatocinsu, sun yi ta yada jita-jitar cewa, matakan kasar Sin sun take hakkokin bil adama.

Sai dai akasin abun da suke nufi, matakan kasar Sin sun cancanci jinjina matuka, domin sun taka rawar gani wajen kare al’umma daga rasa rayukansu sanadiyyar kamuwa da cutar, haka kuma sun kare yaduwar cutar daga kasar zuwa sauran sassan duniya. Gani ya kori ji, domin duk wani dake kasar Sin zai bada shaidar cewa, matakan sun taka rawar gani. Idan kuma aka duba su kasashen masu yada jita jitar, har yanzu ba su kama kafar Sin wajen yaki da cutar ba, haka kuma suna fama da matsalolin tattalin arziki.

Yadda CMG ya shirya wannan taro, hakika zai kara wayar da kan al’ummomin Afrika kan illolin dake tattare da annobar da ma yadda za su kare kawunansu, da kuma dalilan Sin din na daukar matakan da ta dauka, tare da wayar musu da kai daga karai-rayi ko jita-jita da aka yi ta yadawa dangane da su. Baya ga haka, zai zama darasi ta yadda gwamnatocin kasashen za su iya shiryawa tunkarar annoba da mai yuwuwa ka iya barkewa a nan gaba.

Labarai Masu Nasaba

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Duk da cewa, ana ganin Sin ta dauki tsauraran matakai, matakan nata sun haifar da da-mai-ido, ta cimma dimbin nasarori, domin ita ce kasa daya tilo da ta samu ci gaban tattalin arziki bayan bullar annobar, haka kuma ita ce ta bayar da gudunmawa ga ci gaban tattalin arzikin duniya.

Haka zalika, wadannan kyawawan manufofi ne ya sa ake ganin yayin da ci gaban kasashen duniya zai gamu da cikas a shekarar 2023, an yi hasashen tattalin arzikin kasar Sin zai farfado tare da kara kuzari. Ingantattun manufofin kudi da Sin ta dauka da kuma saukaka matakan yaki da annobar da ta yi a baya-bayan nan, za su taimaka wajen samun habakar tattalin arzikinta wanda zai ci gaba da bayar da gudunmawa ga tattalin arzikin duniya baki daya. Haka kuma, zai kara bunkasa harkokin cinikayya da mu’amala da ma musaya da kasashe masu tasowa aminanta, musammam ma na Afrika.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Kasar Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Cote d’Ivoire

Next Post

Sinawa Suna Tinkarar COVID-19 Da Karfin Gwiwa

Related

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

34 minutes ago
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

22 hours ago
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
Daga Birnin Sin

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

23 hours ago
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

1 day ago
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

2 days ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

2 days ago
Next Post
Sinawa Suna Tinkarar COVID-19 Da Karfin Gwiwa

Sinawa Suna Tinkarar COVID-19 Da Karfin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Sin Ta Kalubalanci Kasashen Yammacin Duniya Da Su Tuna Da Laifinsu Na Mulkin Mallaka

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.