• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sinawa Suna Tinkarar COVID-19 Da Karfin Gwiwa

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sinawa Suna Tinkarar COVID-19 Da Karfin Gwiwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu abokai sun rubuta mana sakonni a kwanan baya, inda suka tambaye ni kan yanayin da ake ciki a nan kasar Sin, a fannin tinkarar cutar COVID-19. Amsa ita ce, wata sabuwar barkewar cutar nau’in Omicron ta haifar da wasu matsaloli, sai dai ba ta girgiza karfin gwiwar Sinawa ba.

A yayin barkewar nau’in Omicron ta wannan karo, birnin Beijing, inda nake zaune, yana daga cikin wuraren da suka fi fama da yaduwar annobar. Wasu makwabta da abokaina da yawa sun kamu da ita, inda suka fara zazzabi da tari. Ko da yake galibin mutanen da suka kamu da cutar, alamun da suka nuna ba su da tsanani. Amma saboda dimbin mutanen da suka kamu da cutar ake samu a lokaci guda, ya sa an samu cukuson mutane a asibitoci, da karancin wasu magunguna a shagunan sayar da magani.

  • Sin Ta Sha Alwashin Kare Hakkokinta A Gabar Da Amurka Ta Sake Kakabawa Karin Kamfanonin Sin Takunkumi

Ban da wannan kuma, don magance yin cudanya da mutane masu dauke da kwayoyin cutar COVID-19, jama’a sun daina zuwa sayen kayayyakin abinci da na masarufi a kasuwanni, maimakon haka, sun karkata ga shafukan sayar da kayayyaki na yanar gizo ta Internet gaba daya, lamarin da ya sa ake fuskantar matsalar karancin ma’aikatan jigilar kaya. Don haka yanzu a kan jira karin wasu kwanaki, kafin a iya samun kayan da aka saya ko oda.

To, wadannan su ne matsalolin da ake fuskanta a halin yanzu. Sai dai Sinawa ba su damu sosai ba, ganin yadda suka fara daukar wasu matakai don tinakarar matsalolin. Misali, an bude wuraren ganin likita na wucin gadi, don biyan bukatar mutanen da suke neman ganin likita. Kana an kayyade yawan magunguna da za a iya saya a lokaci guda, ta yadda kowa zai iya samun maganin da yake bukata cikin gaggawa. Ban da wannan kuma, an tura karin ma’aikatan jigilar kayayyaki zuwa wuraren da suka fi fama da annoba, da sanya galibin mutane yin aiki daga gida don magance duk wata kafa ta yaduwar cuta, da lallashin mutane don su huta a gida maimakon zuwa asibiti, idan alamunsu ba su da tsanani.

To, tambaya ita ce, me ya sa Sinawa basa damuwa, ko da yake cutar COVID-19 na yaduwa cikin sauri?

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Saboda sun san matsalar ba za ta dade ba, musamman ma a fannin tattalin arziki. Cikin shekaru 3 da suka wuce, kasar Sin ta yi kokarin daukar tsauraran matakai na hana yaduwar cutar COVID-19, kamar takaita zirga-zirga, da umartar ‘yan kasa don yin gwaji, da killace wadanda suka kamu da cutar har zuwa lokacin da suka warke, da dai sauransu, don kare lafiyar jama’ar kasar, ko da yake matakan na haifar da matsi a fannin tattalin arizki. Amma duk da haka, matakan ba su hana ci gaban tattalin arzikin kasar Sin ba, inda matsakaiciyar karuwar GDPn kasar cikin wadannan shekaru 3 ta kai kashi 4.6%, gaba da na sauran manyan kasashe irinsu Amurka, da Japan, da Jamus, da Faransa. Sa’an nan zuwa wannan lokacin da muke ciki, kasar Sin ta daidaita manufarta ta kandagarkin yaduwar cuta, inda ta sassauta wasu matakan kayyadewa, bisa la’akari da sabon yanayin da aikin tinkarar cutar ke ciki. Hakan ya sa ‘yan kasar ke sa ran ganin karuwar tattalin arizkin Sin cikin karin sauri, bayan da yanayin bazuwar nau’in Omicron na cutar na wannan karo ya kai karshe.

Sa’an nan, wani dalili na daban da ya kawar da damuwar Sinawa, shi ne amincewarsu kan gwamnatin kasar. Sun fahimci dabarar gwamnatin a fannin tsara manufofi: Ta kan tsara wata manufa bisa hakikanin yanayin da kasar ke ciki, da kokarin daidaita manufar a kai a kai, bisa sauyawar sharadi. Ganin yadda kasar Sin ke da tsoffin da yawansu ya kai fiye da kashi 17% na yawan al’ummarta, wadanda kuma suka fi fuskantar hadari idan sun kamu da cutar COVID-19, ya sa kasar daukar tsauraran matakai na dakile cutar cikin shekaru 3 da suka wuce. Sa’an nan zuwa yanzu, yadda fiye da kashi 91% na tsoffin kasar suka riga suka karbi allurar rigakafin cutar, da yadda karfin yaduwar cutar nau’in Omicron ke karuwa, amma kuma karfinta na haddasa mutuwa ke raguwa, sun sa gwamnatin kasar Sin samun damar daidaita manufarta ta kandagarkin cutar.

Duk wata manufa da aka dauka a kasar Sin, jama’ar kasar na da cikakken karfin gwiwa kan cewar, gwamnati za ta kare moriyar daukacin al’ummar kasar, bisa akidarta ta kokarin bautawa jama’a. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matakan Sin Na Yaki Da COVID-19 Sun Haifar Da Da Mai Ido

Next Post

Hisbah Ta Cafke Samari Da ‘Yanmata 19 Wurin Auren Luwadi A Kano

Related

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

11 hours ago
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

12 hours ago
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori
Daga Birnin Sin

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

13 hours ago
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

15 hours ago
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

16 hours ago
UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

1 day ago
Next Post
Hisbah Ta Cafke Samari Da ‘Yanmata 19 Wurin Auren Luwadi A Kano

Hisbah Ta Cafke Samari Da 'Yanmata 19 Wurin Auren Luwadi A Kano

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.