• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matan Tubabbun ‘Yan Boko Haram Sun Haifi Jarirai 262 A Wata 4 Kacal

by Bello Hamza
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Matan Tubabbun ‘Yan Boko Haram Sun Haifi Jarirai 262 A Wata 4 Kacal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayani ya nuna cewa, matan tubabbun ‘yan ta’addan Boko Haram da na ‘yan kungiyar ISWAP da ke zaune a sansanin Hajj Camp da ke Maiduguri babban birnin Jihar Borno sun haifi jarirai 262 a cikin wata 4 kacal da suka gabata.

‘Yan ta’addan dai na rayuwa ne a cikin kananan gidajen da suka gina a cikin sansanin tare da mata da yaransu inda suke gudanar da rayuwa ba tare da wata mastala ba. Ana samun labarin haihuwa a kai kai a tsakanin iyalan tubabban ‘yan ta’addan.

  • Jirgin C919 Na Kasar Sin Ya Samu Amincewar Kara Kera Shi
  • CMG Ya Lashe Lambobin Yabo 4 Na Watsa Shirye-shirye Na Gasar Wasannin Olympics Ta Beijing 2022

Sansanin Hajj Camp na daya daga cikin sansanin hudu da gwamnati ta gina don killace ‘yan ta’addan da suka mika wuya ga dakarun Nijeriya a fagen fama.

Kididdigar ya nuna cewa, cikin jariran da aka haifa akwai mata 150 da maza 112. A watan Yuli na wannan shekarar an haifi yara 94 a sansanin yayin da aka haifi yara 98 a watan Agusta, an kuma haifi jarirai 60 a watan Satumba yayin da aka haifi jarirai 11 a watan Oktoba, kamar yadda kididdigar hukumar da ke kula da sansanin ta bayyana.

Mai kula da dakin shan maganin sansanin na Hajj Camp, Dakta Mohammed Sale ya sanar da haka a ziyarar da tawagar bincike suna kai masa.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Da aka tambaye shi ko an taba samun mace-macen jarirai ko kuma matsalar da ta shafi haihuwa? Saioya bayyana cewa, ba su taba samun wata matsala ba, kuma duk wani aiki da ya fi karfinsu suna mika shi ne ga babban asibiti jihar mai suna’ Umoru Shehu Specialist Hospital’ ko kuma asibitin koyarswa na jami’ar Maiduguri.

Bayani ya nuna cewa,a daidai ranar 11 ga watan Nuwamba na shekarar 2022, mutanen da ke zaune a sansanin sun kai 14,804, Maza sun kai 5,200 kuma dukkan su mayaka ‘yan ta’adda ne, jami’an tsaro sun kashe ire-irensu da dama a yankin arewa maso gabas suma ‘yan ta’adda sun kashe al’umma da dama a yankin arewa maso gabas da suka hada da Borno, Yobe da Adamawa.

Daga cikin tubabbun ‘yan Boko Haram din da ke a sasanin na Hajj Camp, 3,427 na zaune ne da matansu yayin da 1,773 basa tare da matan su. Akwai matan aure 4,443 a sansanin. Wannan bayan wasu matan da ke zaune a sauran sansani uku da ke a wasu sassan jihar.

Bayani ya kuma nuna cewa akwai yara fiye da 5,170 a sansanin na Hajj Camp, maza 2,691 mata 2,479.

Mai bayar da shawara na musamman ga gwamnan Borno a kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Abdullahi Sabi Ishak (Mai Ritaya) ya bayyana cewa, fiye da tubbbabun mayakan 3,500 ne gwammnati ta mayar dasu a cikin al’umma, suna can sun cigaba da harkokin rayuwarsu.

Ita kuwa Kwamishinar Harkokin Mata ta Jihar Borno, Hajiya Zuwaira Gambo, ta bayyana cewa, gwamnati na samarwa tubabbun mayakan magungunan kula da lafiyar kwakwalwa da kuma tallafin bunkasa rayuwarsu, haka kumma ana samu tallafin daga gwamnatin tarayya da wasu kungiyoyi masu bayar da tallafi daga kasashen waje.

A nasa gudummawar, Shehun Borno Dakta Abubakar Umar Garbai ya nuna jin dadinsa ga kokarin jami’an tsaro a yankin, ya ce a halin yanzu babu wani yankin karammar hukuma da ke a hannun mayakan Boko Haram.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramHaihuwaJarirai
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Muradun CAN Da Na Dattawan Arewa A Sikeli

Next Post

Jerin Kayayyakin Da INEC Ta Yi Asara Bayan Kai Mata Hare-hare A Ofisoshinta

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

11 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

18 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

21 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

22 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

1 day ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

1 day ago
Next Post
Jerin Kayayyakin Da INEC Ta Yi Asara Bayan Kai Mata Hare-hare A Ofisoshinta

Jerin Kayayyakin Da INEC Ta Yi Asara Bayan Kai Mata Hare-hare A Ofisoshinta

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.