• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matar Marigayi Abba Kyari Ta Zama Gimbiyar Jama’are Ta Farko

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Abba Kyari

A jiya Lahadi ne mai martaba Sarkin Jama’are, Alhaji Nuhu Muhammadu Wabi ya nada matar tsohon shugaban ma’aikatar fadar shugaban kasa a karkashin Muhammadu Buhari, marigayi Abba Kyari, Hajiya Hauwa Kulu Abba Kyari a matsayin ‘Gimbiyar Masarautar Jama’are’ ta farko.

Da ya ke jawabi a wajen wankan sarautar a fadarsa, Sarkin Jama’are, Nuhu Muhammadu Wabi ya misalta Hajiya Hauwa Kulu a matsayin diya ta kwarai ga masarautar wacce ta bada gagarumin gudunmawarta wajen bunkasawa da inganta cigaban masarautar Jama’are.

  • Manyan Makaratun Jihar Bauchi Sun Ayyana Yajin Aikin Gargadi Na Mako 2

A cewar Sarkin, Girmbiyar za ta taimaka sosai wajen kara kusanto da mata su samu hanyoyin magana kai tsaye da masarautar domin tabbatar da ci gaba mai ma’ana, “Da wannan nadin na Gimbiyar Jama’are ta farko, yanzu matan Jama’are sun samu wakilci a cikin masarautar kuma za a ke jin muryoyinsu.”

Abba Kyari

Ya ce cikin farin ciki a yanzu yana da diya ta kwarai a cikin Majalisar masarautar Jama’are. Jajircewa mace ce wacce ta damu da maida hankali kan cigaba kuma ta bada gagarumar gudunmawa wajen cigaban masarautar Jama’are.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

Sarkin ya kara da cewa, “Bisa irin rawar da ta taka wajen cigaban masarautar Jama’are da ma wadanda take kan yi, suka sa muka nata Gimbiyar masarautar nan. Don haka muna fatan wasu gudunmawar daga gareta yanzu da nauyi ya karu a kafadunta”.

A dan gajeren jawabinta bayan nadin, Gimbiyar masarautar Jama’are ta farko, Hauwa Kulu Abba Kyari ta gode wa Sarkin bisa wannan karamcin da ya mata da ya zo mata a matsayin bazata.

Ta jaddada aniyarta na kara bada gagarumin gudunmawa domin cigaban masarautar Jama’are da al’ummar masarautar baki daya.

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan wannan nadin, babban Manajan gudanarwa na NNPC, Mele Abba Kyari, ya nuna fatan alkairi ga Gimbiyar Jama’are ta farko, ya nuna fatansa na cewa wannan nadin zai karfafa guiwarta wajen cigaba da taimaka wa masarautar da jama’an Jama’are baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100
Labarai

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi
Labarai

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Next Post
FCTA Za Ta Rushe Gidajen Da Aka Gina A Kan Layin Dogo A Kuje Ba Tare Da Biyansu Diyya Ba

FCTA Za Ta Rushe Gidajen Da Aka Gina A Kan Layin Dogo A Kuje Ba Tare Da Biyansu Diyya Ba

LABARAI MASU NASABA

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Abba Kyari

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.