• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matar Marigayi Abba Kyari Ta Zama Gimbiyar Jama’are Ta Farko

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Matar Marigayi Abba Kyari Ta Zama Gimbiyar Jama’are Ta Farko
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Lahadi ne mai martaba Sarkin Jama’are, Alhaji Nuhu Muhammadu Wabi ya nada matar tsohon shugaban ma’aikatar fadar shugaban kasa a karkashin Muhammadu Buhari, marigayi Abba Kyari, Hajiya Hauwa Kulu Abba Kyari a matsayin ‘Gimbiyar Masarautar Jama’are’ ta farko.

Da ya ke jawabi a wajen wankan sarautar a fadarsa, Sarkin Jama’are, Nuhu Muhammadu Wabi ya misalta Hajiya Hauwa Kulu a matsayin diya ta kwarai ga masarautar wacce ta bada gagarumin gudunmawarta wajen bunkasawa da inganta cigaban masarautar Jama’are.

  • Manyan Makaratun Jihar Bauchi Sun Ayyana Yajin Aikin Gargadi Na Mako 2

A cewar Sarkin, Girmbiyar za ta taimaka sosai wajen kara kusanto da mata su samu hanyoyin magana kai tsaye da masarautar domin tabbatar da ci gaba mai ma’ana, “Da wannan nadin na Gimbiyar Jama’are ta farko, yanzu matan Jama’are sun samu wakilci a cikin masarautar kuma za a ke jin muryoyinsu.”

Abba Kyari

Ya ce cikin farin ciki a yanzu yana da diya ta kwarai a cikin Majalisar masarautar Jama’are. Jajircewa mace ce wacce ta damu da maida hankali kan cigaba kuma ta bada gagarumar gudunmawa wajen cigaban masarautar Jama’are.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

Tinubu Ya Fara Hutun Aiki Na Kwanakin 10 A Faransa Da Birtaniya

Sarkin ya kara da cewa, “Bisa irin rawar da ta taka wajen cigaban masarautar Jama’are da ma wadanda take kan yi, suka sa muka nata Gimbiyar masarautar nan. Don haka muna fatan wasu gudunmawar daga gareta yanzu da nauyi ya karu a kafadunta”.

A dan gajeren jawabinta bayan nadin, Gimbiyar masarautar Jama’are ta farko, Hauwa Kulu Abba Kyari ta gode wa Sarkin bisa wannan karamcin da ya mata da ya zo mata a matsayin bazata.

Ta jaddada aniyarta na kara bada gagarumin gudunmawa domin cigaban masarautar Jama’are da al’ummar masarautar baki daya.

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan wannan nadin, babban Manajan gudanarwa na NNPC, Mele Abba Kyari, ya nuna fatan alkairi ga Gimbiyar Jama’are ta farko, ya nuna fatansa na cewa wannan nadin zai karfafa guiwarta wajen cigaba da taimaka wa masarautar da jama’an Jama’are baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Dan Kasuwan Kasar Sin Ya Bullo Da Shirin Magance Matsalar Gurbataccen Ruwa Sha A Nahiyar Afirka

Next Post

FCTA Za Ta Rushe Gidajen Da Aka Gina A Kan Layin Dogo A Kuje Ba Tare Da Biyansu Diyya Ba

Related

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

1 hour ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Fara Hutun Aiki Na Kwanakin 10 A Faransa Da Birtaniya

1 hour ago
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki
Manyan Labarai

Gargaɗi: Ƙauyuka 43 A Jihohi 14 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa 

3 hours ago
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci
Labarai

Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

4 hours ago
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Damfara A Kano

5 hours ago
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno
Manyan Labarai

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

6 hours ago
Next Post
FCTA Za Ta Rushe Gidajen Da Aka Gina A Kan Layin Dogo A Kuje Ba Tare Da Biyansu Diyya Ba

FCTA Za Ta Rushe Gidajen Da Aka Gina A Kan Layin Dogo A Kuje Ba Tare Da Biyansu Diyya Ba

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

September 4, 2025
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai

Tinubu Ya Fara Hutun Aiki Na Kwanakin 10 A Faransa Da Birtaniya

September 4, 2025
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

Gargaɗi: Ƙauyuka 43 A Jihohi 14 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa 

September 4, 2025
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

September 4, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Damfara A Kano

September 4, 2025
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

September 4, 2025
An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

September 4, 2025
An Fara Bincike Kan Ɓarkewar Kwalara A Sokoto – Kwamishina

An Fara Bincike Kan Ɓarkewar Kwalara A Sokoto – Kwamishina

September 4, 2025
Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

September 4, 2025
Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.