• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matar Marigayi Abba Kyari Ta Zama Gimbiyar Jama’are Ta Farko

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Matar Marigayi Abba Kyari Ta Zama Gimbiyar Jama’are Ta Farko
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Lahadi ne mai martaba Sarkin Jama’are, Alhaji Nuhu Muhammadu Wabi ya nada matar tsohon shugaban ma’aikatar fadar shugaban kasa a karkashin Muhammadu Buhari, marigayi Abba Kyari, Hajiya Hauwa Kulu Abba Kyari a matsayin ‘Gimbiyar Masarautar Jama’are’ ta farko.

Da ya ke jawabi a wajen wankan sarautar a fadarsa, Sarkin Jama’are, Nuhu Muhammadu Wabi ya misalta Hajiya Hauwa Kulu a matsayin diya ta kwarai ga masarautar wacce ta bada gagarumin gudunmawarta wajen bunkasawa da inganta cigaban masarautar Jama’are.

  • Manyan Makaratun Jihar Bauchi Sun Ayyana Yajin Aikin Gargadi Na Mako 2

A cewar Sarkin, Girmbiyar za ta taimaka sosai wajen kara kusanto da mata su samu hanyoyin magana kai tsaye da masarautar domin tabbatar da ci gaba mai ma’ana, “Da wannan nadin na Gimbiyar Jama’are ta farko, yanzu matan Jama’are sun samu wakilci a cikin masarautar kuma za a ke jin muryoyinsu.”

Abba Kyari

Ya ce cikin farin ciki a yanzu yana da diya ta kwarai a cikin Majalisar masarautar Jama’are. Jajircewa mace ce wacce ta damu da maida hankali kan cigaba kuma ta bada gagarumar gudunmawa wajen cigaban masarautar Jama’are.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sarkin ya kara da cewa, “Bisa irin rawar da ta taka wajen cigaban masarautar Jama’are da ma wadanda take kan yi, suka sa muka nata Gimbiyar masarautar nan. Don haka muna fatan wasu gudunmawar daga gareta yanzu da nauyi ya karu a kafadunta”.

A dan gajeren jawabinta bayan nadin, Gimbiyar masarautar Jama’are ta farko, Hauwa Kulu Abba Kyari ta gode wa Sarkin bisa wannan karamcin da ya mata da ya zo mata a matsayin bazata.

Ta jaddada aniyarta na kara bada gagarumin gudunmawa domin cigaban masarautar Jama’are da al’ummar masarautar baki daya.

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan wannan nadin, babban Manajan gudanarwa na NNPC, Mele Abba Kyari, ya nuna fatan alkairi ga Gimbiyar Jama’are ta farko, ya nuna fatansa na cewa wannan nadin zai karfafa guiwarta wajen cigaba da taimaka wa masarautar da jama’an Jama’are baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Dan Kasuwan Kasar Sin Ya Bullo Da Shirin Magance Matsalar Gurbataccen Ruwa Sha A Nahiyar Afirka

Next Post

FCTA Za Ta Rushe Gidajen Da Aka Gina A Kan Layin Dogo A Kuje Ba Tare Da Biyansu Diyya Ba

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da É—umi-É—uminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

6 hours ago
Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

7 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya ÆŠaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya ÆŠaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

8 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

11 hours ago
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da ÆŠaliban Kaduna Kyauta A Bas
Labarai

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da ÆŠaliban Kaduna Kyauta A Bas

14 hours ago
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Labarai

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

15 hours ago
Next Post
FCTA Za Ta Rushe Gidajen Da Aka Gina A Kan Layin Dogo A Kuje Ba Tare Da Biyansu Diyya Ba

FCTA Za Ta Rushe Gidajen Da Aka Gina A Kan Layin Dogo A Kuje Ba Tare Da Biyansu Diyya Ba

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya ÆŠaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya ÆŠaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.