ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Makaratun Jihar Bauchi Sun Ayyana Yajin Aikin Gargadi Na Mako 2

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Bauchi

Kwamitin hadaka na manyan makaratun guda biyar da ke jihar Bauchi (JAC), sun ayyana tafiya yajin aikin jan kunne na tsawon kwanaki 14 da zai fara aiki daga ranar Laraba 19 ga watan Yuli zuwa ranar Lahadi 30 ga watan Yulin 2022 domin jawo hankalin Gwamnatin jihar Bauchi da ta share musu hawayensu.

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida a wani taron da suka kira, Shugaban JAC, Abdulkadir Mohammed, ya ce bukatun da suke da su, sun kunshi a gaggauta biyan albashin dukkanin mambobin kungiyar ke bi ba tare da bata wani lokaci ba.

  • 2023: Muna Fata APC Ta Dawo Mulki A Jihar Bauchi -Kwamared Sabo

Wakilinmu ya nakalto cewa hadakar makaratun sun hada da Kwalejin ilimi ta Adamu Tafawa Balewa da ke Kangere da Kwalejin ilimi, koyar da ilimin shari’a da sashin ilimin komai da ruwanka ta A.D Rufa’i da ke Misau da Kwalejin ilimi ta Aminu Saleh da ke garin Azare da Kwalejin Ilimi da  Koyon aikin gona ta jihar Bauchi da kuma babbar Kwalejin Kimiyya, fasaha da kere-kere mallakin gwamantin jihar Bauchi, ATAP.

ADVERTISEMENT

Kazalika, kwamitin ya yi kira da a gaggauta dawo da aiwatar da tsarin karin girma na shekara-shekara ga wadanda suka dace da aka dakatar da yi ba tare da an bayyana a hukumance dalilin dakatarwar ba tun lokacin da gwamnati mai ci ta hau kan mulki.

Shugaban kungiyar ya ce kwamitin nasu ya nuna adawarsa kan shigar da ma’aikata tsarin taimakekeniya ta fansho duk kuwa da cewa hatta ma’aikatan Gwamnatin tarayya ma na kaurace wa tsarin domin wahalar da ke janyo wa ma’aikatan.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

A cewarsa, su na kuma da bukatar a dauki dukkanin matakan da suka dace wajen samar wa mambobin kungiyar rayuwa mai inganci da kuma tsaron hakkokinsu a kowani lokaci domin samun dama da sararin gudanar da aiki ba tare da wani fargaba ko dar-dar ba.

Abdulkadir Mohammed ya ce sun kuma yi adawa da cire wani kaso daga cikin albashin ma’aikatan da sunan shirin tallafin gidauniyar kiwon lafiya da ake kira BASHMA.

Mohammed ya ce bisa wadannan dalilai da sauran hakkokinsu da suke nema ne ya sanya suka zauna suka cimma matsayar tafiya yajin aikin gargadi, kodayake kafin wannan ya ce sun bai wa gwamantin wa’adi da jawo hankalinta tun da jimawa amma matsalolin nasu sai karuwa suke yi. Don haka ne suka ga dacewar tafiya yajin aikin.

Ya cigaba da cewa domin neman adalci dai, sun tuntubi hukumomin da abun ya shafa kan matsalolin nasu domin ganin an yi shawo kan kalubalen da suka hada da Akanta Janar na jihar, da kwamishinan ilimi, da sauran masu ruwa da tsaki kan lamarin amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba, duk da tilin wasikun da suka aike musu.

“Mun rubuta wasika muka aike wa mai girma gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad Abdulkadir a tunanin mu duk abun da suke faruwa bai ma san da su ba. Nan ma dai ba mu samu sauyi ko canji daga matsalolinmu ba.”

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Next Post
Bauchi

'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mai Juna Biyu A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.