ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Makaratun Jihar Bauchi Sun Ayyana Yajin Aikin Gargadi Na Mako 2

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Bauchi

Kwamitin hadaka na manyan makaratun guda biyar da ke jihar Bauchi (JAC), sun ayyana tafiya yajin aikin jan kunne na tsawon kwanaki 14 da zai fara aiki daga ranar Laraba 19 ga watan Yuli zuwa ranar Lahadi 30 ga watan Yulin 2022 domin jawo hankalin Gwamnatin jihar Bauchi da ta share musu hawayensu.

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida a wani taron da suka kira, Shugaban JAC, Abdulkadir Mohammed, ya ce bukatun da suke da su, sun kunshi a gaggauta biyan albashin dukkanin mambobin kungiyar ke bi ba tare da bata wani lokaci ba.

  • 2023: Muna Fata APC Ta Dawo Mulki A Jihar Bauchi -Kwamared Sabo

Wakilinmu ya nakalto cewa hadakar makaratun sun hada da Kwalejin ilimi ta Adamu Tafawa Balewa da ke Kangere da Kwalejin ilimi, koyar da ilimin shari’a da sashin ilimin komai da ruwanka ta A.D Rufa’i da ke Misau da Kwalejin ilimi ta Aminu Saleh da ke garin Azare da Kwalejin Ilimi da  Koyon aikin gona ta jihar Bauchi da kuma babbar Kwalejin Kimiyya, fasaha da kere-kere mallakin gwamantin jihar Bauchi, ATAP.

ADVERTISEMENT

Kazalika, kwamitin ya yi kira da a gaggauta dawo da aiwatar da tsarin karin girma na shekara-shekara ga wadanda suka dace da aka dakatar da yi ba tare da an bayyana a hukumance dalilin dakatarwar ba tun lokacin da gwamnati mai ci ta hau kan mulki.

Shugaban kungiyar ya ce kwamitin nasu ya nuna adawarsa kan shigar da ma’aikata tsarin taimakekeniya ta fansho duk kuwa da cewa hatta ma’aikatan Gwamnatin tarayya ma na kaurace wa tsarin domin wahalar da ke janyo wa ma’aikatan.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

A cewarsa, su na kuma da bukatar a dauki dukkanin matakan da suka dace wajen samar wa mambobin kungiyar rayuwa mai inganci da kuma tsaron hakkokinsu a kowani lokaci domin samun dama da sararin gudanar da aiki ba tare da wani fargaba ko dar-dar ba.

Abdulkadir Mohammed ya ce sun kuma yi adawa da cire wani kaso daga cikin albashin ma’aikatan da sunan shirin tallafin gidauniyar kiwon lafiya da ake kira BASHMA.

Mohammed ya ce bisa wadannan dalilai da sauran hakkokinsu da suke nema ne ya sanya suka zauna suka cimma matsayar tafiya yajin aikin gargadi, kodayake kafin wannan ya ce sun bai wa gwamantin wa’adi da jawo hankalinta tun da jimawa amma matsalolin nasu sai karuwa suke yi. Don haka ne suka ga dacewar tafiya yajin aikin.

Ya cigaba da cewa domin neman adalci dai, sun tuntubi hukumomin da abun ya shafa kan matsalolin nasu domin ganin an yi shawo kan kalubalen da suka hada da Akanta Janar na jihar, da kwamishinan ilimi, da sauran masu ruwa da tsaki kan lamarin amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba, duk da tilin wasikun da suka aike musu.

“Mun rubuta wasika muka aike wa mai girma gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad Abdulkadir a tunanin mu duk abun da suke faruwa bai ma san da su ba. Nan ma dai ba mu samu sauyi ko canji daga matsalolinmu ba.”

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Bauchi

'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mai Juna Biyu A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.