• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matarka Daya Ta Isheka…

by Ibrahim Bala
2 years ago
Matarka

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Jama’a barkanku da kasancewa tare da wannan fili mai albarka, filin da nake kawo muku batutuwan da suke ci mun tuwo a kwarya, wanda a yau ma ina tafe da wani batun wanda nake son jan hankali akai musamman ga maza.

 Idan muka yi duba da yanayin da muke ciki na rayuwarmu, musamman a arewacin Nageriya ko na ce Hausawanmu, za mu ga yadda rayuwar Malan bahaushe ke tafiya a yanzu, misali; mutum ne yake a gidan haya, yanada mata guda daya, da kuma yaronsa daya ko biyu, ya kan dan biya musu kudin makaranta a hankali, wal’alla ya samu dan dama ya siyi babur din hawa ko makamancin hakan cikin rufin asiri, ya kan dan ci da su da safe, rana, da kuma dare, har cikin ikon Allah za a ga ya dan samu abin da za a kai baki na kwadayi da sauransu.

Sai dai wata dabi’a irin ta Malan Bahaushe wadda take zama tushen matsala a zamantakewar rayuwa, duk da kasancewarsa cikin irin wannan hali, hakan baya iya hana shi yawan aure-aure. Da zarar ya dan samu wasu dan kudin saman kudin da yake samu, madadin ya tsaya ya tsarawa kansa rayuwa ta yadda zai taimaki kansa da kuma iyalinsa, kan abin da zai amfane su a gaba kamar dai; Gina gida, Siyan fili, ko canja sana’a me gwabi, ko kara jari, ko makamancin haka, amma ina! sai ya je ya kara aure, wanda hakan yana daya daga cikin abubuwan da suke janyo tabarbarewar zamantakewar aure, har ta kai ga an samu matsala a tsakanin iyali.

Sai dai wani hanzari ba gudu ba, na kan rasa gane irin wannan hali na Malan Bahaushe game da yawan aure-aure, wai shin hakan dabi’a ce ko kuwa gasa ce?

LABARAI MASU NASABA

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 

Mu yi hakuri mana saurin me muke yi?, ya kamata a kiyaye, kuma ayi adalci, idan ka san ba za ka iya yin adalci ba to, kayi hakuri da matarka guda daya da ‘ya’yanka.

Ya kamata a rinka sara ana duban bakin gatari, ta yadda idan aka ga wani ya yi mata uku wal’alla yanada wadatar da zai yi mata ukunne, madadin ace kana gidan haya ka auri mace daya, ka auri biyu, kayi ta uku, kuma kana harin ta hudu, shin me yake damunka?

Yanada kyau iyayen da suke bayar da ‘ya’yansu aure, su rinka yin hakuri wajen yin buncike da kyau, idan suka tabbatar da mutum zai auri ‘yarsu yanada mata biyu duk a gidan haya to, bai kamata a bashi auren ba duk rufin asirinsa. Ba dan komai ba, sai dan gudun abun da yake juyawa ya zamo ba nasa ba, wannan zalama ce da kuma hadama.

Haka ma matan da suka tsinci kansu a irin wannan yanayin, su yi hakuri, muddin mijin yana iya sauke nauyin matar da Allah ya dora masa a kanshi to, ta zauna, kada a zugata ta fita. Tunda in ma ta fita ba a san inda za ta je ba, ina kuma kara kira ga ‘yan uwana maza cewar; dan Allah mu rinka yin hakuri, auren nan fa ba dole sai ka yi biyu ko uku ba, matarka daya ta ishe ka, biyun fa cewa aka yi idan za ka yi adalci, uku sai za ka yi adalci, hudu sai za ka yi adalci, daya ce aka ce maka ka yi.

Da wannan nake kara jan hankali cewa; dan Allah kodan zaman lafiyarmu da iyalanmu da ‘ya’yanmu, saboda baka san inda ‘ya’yanka za su je ba, sai ka ga mutum ya je ya haifi ‘ya’ya kusan goma sha, matamsa kowacce gidanta daban-daban haya ake biya, ina dalilin irin wannan?

Mu yi wa kanmu fada mana, mu tsaya mu tsarawa kanmu rayuwar da ba za mu sha wahala ba.

Wassalamu Alaikum.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)

December 29, 2024
Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 

December 21, 2024
Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba
Marurun Zuciya

Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba

May 12, 2024
Next Post
Mutane Miliyan 13.517 Sun Shiga Ko Fita Daga Kasar Sin A Lokacin Hutun Bikin Bazara

Mutane Miliyan 13.517 Sun Shiga Ko Fita Daga Kasar Sin A Lokacin Hutun Bikin Bazara

LABARAI MASU NASABA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Matarka

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.