• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matarka Daya Ta Isheka…

by Ibrahim Bala
2 years ago
Matarka

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Jama’a barkanku da kasancewa tare da wannan fili mai albarka, filin da nake kawo muku batutuwan da suke ci mun tuwo a kwarya, wanda a yau ma ina tafe da wani batun wanda nake son jan hankali akai musamman ga maza.

 Idan muka yi duba da yanayin da muke ciki na rayuwarmu, musamman a arewacin Nageriya ko na ce Hausawanmu, za mu ga yadda rayuwar Malan bahaushe ke tafiya a yanzu, misali; mutum ne yake a gidan haya, yanada mata guda daya, da kuma yaronsa daya ko biyu, ya kan dan biya musu kudin makaranta a hankali, wal’alla ya samu dan dama ya siyi babur din hawa ko makamancin hakan cikin rufin asiri, ya kan dan ci da su da safe, rana, da kuma dare, har cikin ikon Allah za a ga ya dan samu abin da za a kai baki na kwadayi da sauransu.

Sai dai wata dabi’a irin ta Malan Bahaushe wadda take zama tushen matsala a zamantakewar rayuwa, duk da kasancewarsa cikin irin wannan hali, hakan baya iya hana shi yawan aure-aure. Da zarar ya dan samu wasu dan kudin saman kudin da yake samu, madadin ya tsaya ya tsarawa kansa rayuwa ta yadda zai taimaki kansa da kuma iyalinsa, kan abin da zai amfane su a gaba kamar dai; Gina gida, Siyan fili, ko canja sana’a me gwabi, ko kara jari, ko makamancin haka, amma ina! sai ya je ya kara aure, wanda hakan yana daya daga cikin abubuwan da suke janyo tabarbarewar zamantakewar aure, har ta kai ga an samu matsala a tsakanin iyali.

Sai dai wani hanzari ba gudu ba, na kan rasa gane irin wannan hali na Malan Bahaushe game da yawan aure-aure, wai shin hakan dabi’a ce ko kuwa gasa ce?

LABARAI MASU NASABA

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 

Mu yi hakuri mana saurin me muke yi?, ya kamata a kiyaye, kuma ayi adalci, idan ka san ba za ka iya yin adalci ba to, kayi hakuri da matarka guda daya da ‘ya’yanka.

Ya kamata a rinka sara ana duban bakin gatari, ta yadda idan aka ga wani ya yi mata uku wal’alla yanada wadatar da zai yi mata ukunne, madadin ace kana gidan haya ka auri mace daya, ka auri biyu, kayi ta uku, kuma kana harin ta hudu, shin me yake damunka?

Yanada kyau iyayen da suke bayar da ‘ya’yansu aure, su rinka yin hakuri wajen yin buncike da kyau, idan suka tabbatar da mutum zai auri ‘yarsu yanada mata biyu duk a gidan haya to, bai kamata a bashi auren ba duk rufin asirinsa. Ba dan komai ba, sai dan gudun abun da yake juyawa ya zamo ba nasa ba, wannan zalama ce da kuma hadama.

Haka ma matan da suka tsinci kansu a irin wannan yanayin, su yi hakuri, muddin mijin yana iya sauke nauyin matar da Allah ya dora masa a kanshi to, ta zauna, kada a zugata ta fita. Tunda in ma ta fita ba a san inda za ta je ba, ina kuma kara kira ga ‘yan uwana maza cewar; dan Allah mu rinka yin hakuri, auren nan fa ba dole sai ka yi biyu ko uku ba, matarka daya ta ishe ka, biyun fa cewa aka yi idan za ka yi adalci, uku sai za ka yi adalci, hudu sai za ka yi adalci, daya ce aka ce maka ka yi.

Da wannan nake kara jan hankali cewa; dan Allah kodan zaman lafiyarmu da iyalanmu da ‘ya’yanmu, saboda baka san inda ‘ya’yanka za su je ba, sai ka ga mutum ya je ya haifi ‘ya’ya kusan goma sha, matamsa kowacce gidanta daban-daban haya ake biya, ina dalilin irin wannan?

Mu yi wa kanmu fada mana, mu tsaya mu tsarawa kanmu rayuwar da ba za mu sha wahala ba.

Wassalamu Alaikum.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)

December 29, 2024
Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 

December 21, 2024
Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba
Marurun Zuciya

Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba

May 12, 2024
Next Post
Mutane Miliyan 13.517 Sun Shiga Ko Fita Daga Kasar Sin A Lokacin Hutun Bikin Bazara

Mutane Miliyan 13.517 Sun Shiga Ko Fita Daga Kasar Sin A Lokacin Hutun Bikin Bazara

LABARAI MASU NASABA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.