ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matarka Daya Ta Isheka…

by Ibrahim Bala
2 years ago
Matarka

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Jama’a barkanku da kasancewa tare da wannan fili mai albarka, filin da nake kawo muku batutuwan da suke ci mun tuwo a kwarya, wanda a yau ma ina tafe da wani batun wanda nake son jan hankali akai musamman ga maza.

 Idan muka yi duba da yanayin da muke ciki na rayuwarmu, musamman a arewacin Nageriya ko na ce Hausawanmu, za mu ga yadda rayuwar Malan bahaushe ke tafiya a yanzu, misali; mutum ne yake a gidan haya, yanada mata guda daya, da kuma yaronsa daya ko biyu, ya kan dan biya musu kudin makaranta a hankali, wal’alla ya samu dan dama ya siyi babur din hawa ko makamancin hakan cikin rufin asiri, ya kan dan ci da su da safe, rana, da kuma dare, har cikin ikon Allah za a ga ya dan samu abin da za a kai baki na kwadayi da sauransu.

ADVERTISEMENT

Sai dai wata dabi’a irin ta Malan Bahaushe wadda take zama tushen matsala a zamantakewar rayuwa, duk da kasancewarsa cikin irin wannan hali, hakan baya iya hana shi yawan aure-aure. Da zarar ya dan samu wasu dan kudin saman kudin da yake samu, madadin ya tsaya ya tsarawa kansa rayuwa ta yadda zai taimaki kansa da kuma iyalinsa, kan abin da zai amfane su a gaba kamar dai; Gina gida, Siyan fili, ko canja sana’a me gwabi, ko kara jari, ko makamancin haka, amma ina! sai ya je ya kara aure, wanda hakan yana daya daga cikin abubuwan da suke janyo tabarbarewar zamantakewar aure, har ta kai ga an samu matsala a tsakanin iyali.

Sai dai wani hanzari ba gudu ba, na kan rasa gane irin wannan hali na Malan Bahaushe game da yawan aure-aure, wai shin hakan dabi’a ce ko kuwa gasa ce?

LABARAI MASU NASABA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

Mu yi hakuri mana saurin me muke yi?, ya kamata a kiyaye, kuma ayi adalci, idan ka san ba za ka iya yin adalci ba to, kayi hakuri da matarka guda daya da ‘ya’yanka.

Ya kamata a rinka sara ana duban bakin gatari, ta yadda idan aka ga wani ya yi mata uku wal’alla yanada wadatar da zai yi mata ukunne, madadin ace kana gidan haya ka auri mace daya, ka auri biyu, kayi ta uku, kuma kana harin ta hudu, shin me yake damunka?

Yanada kyau iyayen da suke bayar da ‘ya’yansu aure, su rinka yin hakuri wajen yin buncike da kyau, idan suka tabbatar da mutum zai auri ‘yarsu yanada mata biyu duk a gidan haya to, bai kamata a bashi auren ba duk rufin asirinsa. Ba dan komai ba, sai dan gudun abun da yake juyawa ya zamo ba nasa ba, wannan zalama ce da kuma hadama.

Haka ma matan da suka tsinci kansu a irin wannan yanayin, su yi hakuri, muddin mijin yana iya sauke nauyin matar da Allah ya dora masa a kanshi to, ta zauna, kada a zugata ta fita. Tunda in ma ta fita ba a san inda za ta je ba, ina kuma kara kira ga ‘yan uwana maza cewar; dan Allah mu rinka yin hakuri, auren nan fa ba dole sai ka yi biyu ko uku ba, matarka daya ta ishe ka, biyun fa cewa aka yi idan za ka yi adalci, uku sai za ka yi adalci, hudu sai za ka yi adalci, daya ce aka ce maka ka yi.

Da wannan nake kara jan hankali cewa; dan Allah kodan zaman lafiyarmu da iyalanmu da ‘ya’yanmu, saboda baka san inda ‘ya’yanka za su je ba, sai ka ga mutum ya je ya haifi ‘ya’ya kusan goma sha, matamsa kowacce gidanta daban-daban haya ake biya, ina dalilin irin wannan?

Mu yi wa kanmu fada mana, mu tsaya mu tsarawa kanmu rayuwar da ba za mu sha wahala ba.

Wassalamu Alaikum.

Matarka
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

MASU ALAKA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
Marurun Zuciya

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Marurun Zuciya

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

May 23, 2026
marayu
Marurun Zuciya

Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

May 17, 2026
Next Post
Mutane Miliyan 13.517 Sun Shiga Ko Fita Daga Kasar Sin A Lokacin Hutun Bikin Bazara

Mutane Miliyan 13.517 Sun Shiga Ko Fita Daga Kasar Sin A Lokacin Hutun Bikin Bazara

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.