ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba

by Ibrahim Bala
2 years ago
Barace

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Barkan ku da wannan lokaci, cikin filinmu na MARURUN ZUCIYA, fili na musamman wanda muke tattaunawa a kan abubuwan da suke ci wa al’umma tuwo a kwarya, kamar kowane mako yau ma filin na tafe da wani batun da za mu yi magana a kai.

A wannan karan zan yi magana ne a kan barace-barace, alal hakika kowa ya riga ya sani babu kyau, kuma a yadda masana masu ilimi suke fada cewar; yawan barace-barace yana kawo talauci.

ADVERTISEMENT

Wanda a arewacin Najeriya abun ya zo da sabon salo ta hanyar yin bara ta ko’ina, ba namiji ba mace, ba babba ba yaro, ba tsoho ba tsohuwa, ba budurwa ba saurayi, bara ta zo da abubuwa kala daban-daban, wasu ma ba za su kwatantu ba. Shin ta ina za mu magance wannan matsalar?

Kira na ga dukkanin wanda ya ke da, ikon fada a ji ko gyarawa a arewacinmu daya kalli al’amarin da idon basira, domin gaba abun ba zai haifar da da mai ido ba. Shin ta ya za mu magance wannan matsalar?

LABARAI MASU NASABA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

Abun dubawa da nazari shi ne; idan za ka taimaki dan wani to, ka sani danka ka taimaka. Domin idan kana magidanci kana ganin ‘ya’yanka kawai ka ke taimakawa to, wadanda baka taimakawa ba su ne fa abokan ‘ya’yanka, idan wadannan yaran baka yi kokarin hanasu bara ba to, wataran kai ma za ka iya mutuwa ba tare da ka samu me taimakawa danka ba, haka rayuwa take, amma idan ka gina wani to, shi ma zai zo ya taimaki danka.

Ni ina ganin ta hanyoyin da za a magance bara banda gwamnati, ba iya gwamnati ce kadai za ta magance yawan barace-baracen nan ba, mu kalli al’amarin, idan yunwa ce da fatara da halin da a ke ciki na wannan yanayi shi ne; Idan marayu ne mu dauki gabar taimakawa marayu ta gidaje, idan abinci ne mu taimaka musu da abinci, idan kuma babu marayun to, mu kalli almajirai koda mutum daya ne mu dauki kwano ya rika bawa kowanne almajiri, domin abun yayi yawa.

Mu kalli hanyoyi da gabobi ta yadda za mu magance wannan matsalolin gaskiya abun kunya ne, gaba abun ba zai haifar mana da abu mai kyau ba, saboda kullum abun sake gaba ya ke yi, kara rubanya ya ke, manyanmu da shuwagabanninmu su kuma sun ki kallon abun a matsayin wani al’amari ne da zai iya shafar arewa kuma ya ba mu matsala nan gaba.

Idan ka yi taimako kanka da ‘ya’yanka ka taimaka, Allah ya tsare mu ya kare mu, Allah ya kawo mana mafita cikin wannan al’amarin.

Barace
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

MASU ALAKA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
Marurun Zuciya

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Marurun Zuciya

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

May 23, 2026
marayu
Marurun Zuciya

Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

May 17, 2026
Next Post
Gimbiyoyin Kannywood (1)

Gimbiyoyin Kannywood (1)

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.