ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba

by Ibrahim Bala
2 years ago
Barace

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Barkan ku da wannan lokaci, cikin filinmu na MARURUN ZUCIYA, fili na musamman wanda muke tattaunawa a kan abubuwan da suke ci wa al’umma tuwo a kwarya, kamar kowane mako yau ma filin na tafe da wani batun da za mu yi magana a kai.

A wannan karan zan yi magana ne a kan barace-barace, alal hakika kowa ya riga ya sani babu kyau, kuma a yadda masana masu ilimi suke fada cewar; yawan barace-barace yana kawo talauci.

ADVERTISEMENT

Wanda a arewacin Najeriya abun ya zo da sabon salo ta hanyar yin bara ta ko’ina, ba namiji ba mace, ba babba ba yaro, ba tsoho ba tsohuwa, ba budurwa ba saurayi, bara ta zo da abubuwa kala daban-daban, wasu ma ba za su kwatantu ba. Shin ta ina za mu magance wannan matsalar?

Kira na ga dukkanin wanda ya ke da, ikon fada a ji ko gyarawa a arewacinmu daya kalli al’amarin da idon basira, domin gaba abun ba zai haifar da da mai ido ba. Shin ta ya za mu magance wannan matsalar?

LABARAI MASU NASABA

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

Abun dubawa da nazari shi ne; idan za ka taimaki dan wani to, ka sani danka ka taimaka. Domin idan kana magidanci kana ganin ‘ya’yanka kawai ka ke taimakawa to, wadanda baka taimakawa ba su ne fa abokan ‘ya’yanka, idan wadannan yaran baka yi kokarin hanasu bara ba to, wataran kai ma za ka iya mutuwa ba tare da ka samu me taimakawa danka ba, haka rayuwa take, amma idan ka gina wani to, shi ma zai zo ya taimaki danka.

Ni ina ganin ta hanyoyin da za a magance bara banda gwamnati, ba iya gwamnati ce kadai za ta magance yawan barace-baracen nan ba, mu kalli al’amarin, idan yunwa ce da fatara da halin da a ke ciki na wannan yanayi shi ne; Idan marayu ne mu dauki gabar taimakawa marayu ta gidaje, idan abinci ne mu taimaka musu da abinci, idan kuma babu marayun to, mu kalli almajirai koda mutum daya ne mu dauki kwano ya rika bawa kowanne almajiri, domin abun yayi yawa.

Mu kalli hanyoyi da gabobi ta yadda za mu magance wannan matsalolin gaskiya abun kunya ne, gaba abun ba zai haifar mana da abu mai kyau ba, saboda kullum abun sake gaba ya ke yi, kara rubanya ya ke, manyanmu da shuwagabanninmu su kuma sun ki kallon abun a matsayin wani al’amari ne da zai iya shafar arewa kuma ya ba mu matsala nan gaba.

Idan ka yi taimako kanka da ‘ya’yanka ka taimaka, Allah ya tsare mu ya kare mu, Allah ya kawo mana mafita cikin wannan al’amarin.

Barace
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Talauci Ba Hujjar Aikata Muggan Laifukka Ba Ne 

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Marurun Zuciya

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

May 23, 2026
marayu
Marurun Zuciya

Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

May 17, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Marurun Zuciya

2027: Bukatar Zaben Shugabanni Na Gari

May 10, 2026
Next Post
Gimbiyoyin Kannywood (1)

Gimbiyoyin Kannywood (1)

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.