• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matasa A Guji Bangar Siyasa, ‘Yan Siyasa Ba Za Su Ba Ku Komai Ba Sai Ƙwaya – Matasan Arewa A Kudu

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
Matasa A Guji Bangar Siyasa, ‘Yan Siyasa Ba Za Su Ba Ku Komai Ba Sai Ƙwaya – Matasan Arewa A Kudu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasancewar matasa ƙashin bayan al’umma wanda kuma suka fi fuskantar haɗarin amfani da su wajen cimma muradun miyagun ‘yan siyasa, Gamayyar Matasan Arewa a Kudu da ke Legas, ta yi kira da babbar murya ga ɗaukacin matasan Nijeriya da kar su bari ɓata-garin ‘yan siyasa su riƙa amfani da su a matsayin ‘yan bangar siyasa musamman a halin yanzu da aka shiga kakar siyasa.
Gamayyar ta yi kiran ne ta hannun shugabanta, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci a wani ɓangare na yunƙurin da take yi wajen wayar wa da ‘yan ƙasa kai a game da abubuwan da za su kawo musu ci gaba a rayuwarsu.

  • Yadda Ango Ya Yi Shahada Wajen Kare Amaryarsa Daga ‘Yan Bindiga

A cewar gamayyar, “muna sake tunatarwa ga dukkan matasan Nijeriya da su guji yin bangar siyasa domin rayuwarsu tana cikin haɗari, ɓata-garin ‘yan siyasar ƙasarmu ba za su tsinana musu komai ba illa su yi ɗibga musu kayan maye saboda gusar da hankulansu, domin sun san cewa idan matasan suna cikin hayyacinsu ba za su iya saka su miyagun abubuwa ba a ƙoƙarinsu na cimma burinsu na son zuciya.”

Ƙungiyar ta ce irin yadda ake amfani da ƙazaman kuɗaɗe wajen tsayar da ‘yan takara a jam’iyyu manuniya ce kan irin lalacewar da tsarin siyasar ƙasar nan ya yi.

“Kun ga dai yadda ake sayen daliget, wannan shi ne ya nuna wa duniya cewa tsarin zaɓenmu ya gurɓace. ‘Yan siyasar sun mayar da sha’anin takara na ko-a-mutu-ko-a-yi-rai, sannan duk abubuwan da suke faruwa a arewa na kisan jama’a da sace-sacen dukiyoyinsu da cin zarafin iyalai akwai alamun wasu da ke kan mulki a madafun ikon gwamnati suna da hannu a ciki, haka nan wasu masu neman tsayawa takara, shi ya sa wasu ko ana-ha-maza-ha-mata za su ce dole su ci zaɓe domin rufe asirin miyagun ayyukansu.

“Kowa ya san arewa tana da arzikin ma’adanai masu daraja, shi ya sa da ake son sacewa sai aka kitsa mana kashe-kashe da sace-sace, kuma abin takaici ba mu da shugabanni nagari da za hana. Shi ya sa a kullum yankin komawa baya yake yi, muna sake kira ga jami’an tsaro da su guji harka da ‘yan siyasa domin amana ce suka ɗauka ta kare al’umma ba wasu tsirarun miyagun mutane ba kawai kuma za su yi wa Allah bayani saboda tsakani da talakawan arewa na cikin mawuyacin hali.” In ji shugaban gamayyar.

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Ƙungiyar ta ce abubuwan da ake yi na rashin kishin ƙasa daga shugabanni ya ƙara sabbaba yunwa, matsalar tsaro da sauran ƙuncin rayuwa, ga kuma abin kunya harkar ilimi ta zama wasa da cin zarafin malaman jami’o’i.

“Yara matasa ‘yan label 400 (ajin ƙarshe) an ɓata musu karatunsu, wasu suna lokacin jarabawa aka rufe jami’o’i, ya kamata shuganinmu nagari su sake jajircewa kuma su ji tsoron Allah su ci gaba da faɗa wa juna gaskiya domin akwai ranar hisabi, abun dubawa a nan a yankin Yarabawa irin waɗannan halayen babu su, haka a yankin Inyamurai, duk inda ka bi mu ‘yan arewa ake kashewa, kuma hakan na ta faruwa tun daga kisan kisan gillar da aka yi wa manyan magabatanmu irin su Sardauna da Tafawa ɓalewa, don haka ya kamata wannan ya zama izina ga duk mai kishin ƙasa.” In ji Galadanci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnonin APC Suna Goyan Bayan Osinbajo A Zaben Fidda Gwani

Next Post

Buhari Ya Sake Shillawa Kasar Ghana Don Halartar Taron ECOWAS

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

5 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

7 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

8 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

9 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

10 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

11 hours ago
Next Post
Buhari Ya Sake Shillawa Kasar Ghana Don Halartar Taron ECOWAS

Buhari Ya Sake Shillawa Kasar Ghana Don Halartar Taron ECOWAS

LABARAI MASU NASABA

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.