ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matasa A Guji Bangar Siyasa, ‘Yan Siyasa Ba Za Su Ba Ku Komai Ba Sai Ƙwaya – Matasan Arewa A Kudu

by yahuzajere
4 years ago
Matasa

Kasancewar matasa ƙashin bayan al’umma wanda kuma suka fi fuskantar haɗarin amfani da su wajen cimma muradun miyagun ‘yan siyasa, Gamayyar Matasan Arewa a Kudu da ke Legas, ta yi kira da babbar murya ga ɗaukacin matasan Nijeriya da kar su bari ɓata-garin ‘yan siyasa su riƙa amfani da su a matsayin ‘yan bangar siyasa musamman a halin yanzu da aka shiga kakar siyasa.
Gamayyar ta yi kiran ne ta hannun shugabanta, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci a wani ɓangare na yunƙurin da take yi wajen wayar wa da ‘yan ƙasa kai a game da abubuwan da za su kawo musu ci gaba a rayuwarsu.

  • Yadda Ango Ya Yi Shahada Wajen Kare Amaryarsa Daga ‘Yan Bindiga

A cewar gamayyar, “muna sake tunatarwa ga dukkan matasan Nijeriya da su guji yin bangar siyasa domin rayuwarsu tana cikin haɗari, ɓata-garin ‘yan siyasar ƙasarmu ba za su tsinana musu komai ba illa su yi ɗibga musu kayan maye saboda gusar da hankulansu, domin sun san cewa idan matasan suna cikin hayyacinsu ba za su iya saka su miyagun abubuwa ba a ƙoƙarinsu na cimma burinsu na son zuciya.”

Ƙungiyar ta ce irin yadda ake amfani da ƙazaman kuɗaɗe wajen tsayar da ‘yan takara a jam’iyyu manuniya ce kan irin lalacewar da tsarin siyasar ƙasar nan ya yi.

ADVERTISEMENT

“Kun ga dai yadda ake sayen daliget, wannan shi ne ya nuna wa duniya cewa tsarin zaɓenmu ya gurɓace. ‘Yan siyasar sun mayar da sha’anin takara na ko-a-mutu-ko-a-yi-rai, sannan duk abubuwan da suke faruwa a arewa na kisan jama’a da sace-sacen dukiyoyinsu da cin zarafin iyalai akwai alamun wasu da ke kan mulki a madafun ikon gwamnati suna da hannu a ciki, haka nan wasu masu neman tsayawa takara, shi ya sa wasu ko ana-ha-maza-ha-mata za su ce dole su ci zaɓe domin rufe asirin miyagun ayyukansu.

“Kowa ya san arewa tana da arzikin ma’adanai masu daraja, shi ya sa da ake son sacewa sai aka kitsa mana kashe-kashe da sace-sace, kuma abin takaici ba mu da shugabanni nagari da za hana. Shi ya sa a kullum yankin komawa baya yake yi, muna sake kira ga jami’an tsaro da su guji harka da ‘yan siyasa domin amana ce suka ɗauka ta kare al’umma ba wasu tsirarun miyagun mutane ba kawai kuma za su yi wa Allah bayani saboda tsakani da talakawan arewa na cikin mawuyacin hali.” In ji shugaban gamayyar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

Ƙungiyar ta ce abubuwan da ake yi na rashin kishin ƙasa daga shugabanni ya ƙara sabbaba yunwa, matsalar tsaro da sauran ƙuncin rayuwa, ga kuma abin kunya harkar ilimi ta zama wasa da cin zarafin malaman jami’o’i.

“Yara matasa ‘yan label 400 (ajin ƙarshe) an ɓata musu karatunsu, wasu suna lokacin jarabawa aka rufe jami’o’i, ya kamata shuganinmu nagari su sake jajircewa kuma su ji tsoron Allah su ci gaba da faɗa wa juna gaskiya domin akwai ranar hisabi, abun dubawa a nan a yankin Yarabawa irin waɗannan halayen babu su, haka a yankin Inyamurai, duk inda ka bi mu ‘yan arewa ake kashewa, kuma hakan na ta faruwa tun daga kisan kisan gillar da aka yi wa manyan magabatanmu irin su Sardauna da Tafawa ɓalewa, don haka ya kamata wannan ya zama izina ga duk mai kishin ƙasa.” In ji Galadanci.

Matasa
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Next Post
Buhari Ya Sake Shillawa Kasar Ghana Don Halartar Taron ECOWAS

Buhari Ya Sake Shillawa Kasar Ghana Don Halartar Taron ECOWAS

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.