• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro Na Ci Gaba Da Fatattakar Al’umma Bayan Cikar Wa’adin Disamba

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Matsalar Tsaro Na Ci Gaba Da Fatattakar Al’umma Bayan Cikar Wa’adin Disamba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da umarnin da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya ba sojojin Nijeriya da sauran jami’an tsaron kasa na su tabbatar da kawo karshen ayyukan ta’addanci a sassan kasar nan tare da dawo da zaman lafiya kafin karshen watan Disamba na shekarar 2022, ayyukan ta’addanci irin su garkuwa da mutane, kashe-kashe suna ci gaba da cin rayukan al’umma a sassan kasar nan ba kakkautawa.

Wato duk da ba a iya kawo karshen kashe-kashen ba amma masana sun tabbatar daan samu raguwar kashe-kashen a cikin watanni 4 da suka wuce.

  • Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Bayyana Aniyar Tallafawa Ci Gaban Fannin Yawon Bude Ido Da Farfado Da Tattalin Arzikin Duniya

Bayani ya nuna cewa, an kashe akalla mutum 671 ciki kuwa da fararen hula, jami’an ‘yansanda dana sojoji tun bayan da Ministan cikin gida, Rauf Aregbesola ya sanar da umarnin na shugaban kasa a taron manema labarai na kasa da kasa da aka yi a watan Satumba na shekarar 2022 na cewa, Shugaba Buhari ya umarci shugabanin rundunonin tsaro su fattataki ‘yan ta’adda su kuma tabbatr da kawo karshen su zuwa karshen shekarar 2022.
Amma abin takaicin shi ne an ci gaba da kashe al’umma tun bayan da wa’adin ya kare. ‘Yansanda 4 sun rasa rayukansu a yayin da ‘yan bindiga suka farmaki tawagar tsohon Gwamnan Jihar Imo Ikedi Ohakim a daidai kauyen Ehime da ke karamar hukumar ta jihar.

Haka kuma, duk da kasancewar sojoji na sintiri a sassan kasar nan amma ‘yan ta’adda sun ci gaba da kai hare-hare tare da sace mutane suna garkuwa da su a jihohin Zamfara, Katsina da Kaduna.
Rahoton da jaridar Daily Trust ta bayar ya nuna cewa, al’ummar Nijeriya sun ci gaba da fuskantar matsaloli daga manyan kungiyoyin ‘yan ta’adda nan kamar su Boko Haram da ISWAP ga kuma rikicin manomja da makiyaya ga kuma ayyukkan ta’addancin ’yann aware na masu neman kafa kasar Biafra (IPOB).
Kididdigar da jaridar Daily Trust ta samar ya nuna cewa, daga cikin mutum 671 da aka kashe a cikin wattani 4 da suka wuce, 614 fararen hula ne, 47 kuma jami’an sojoji ne yayin da 10 daga cikin su jami’an ‘yansanda ne an kuma tabbatar da sace mutun 1,321 a tsakanin watan Satumba zuwa Disamba.
Kashi 80 Na Wadanmda Suka Mutu Da Wadanda Aka Sace Daga Arewa Ne
Daga cikin mutum 614 aka kashe a tsakanin watan Satumba zuwa Disamba na shekarar 2022, bayani ya nuna cewa, kashi 85 na wadanda suka mutu an kashe su ne a yankin arewacin Nijeriya yayin da kashi 15 ne suka fito daga kudancin kasar. Bayanin ya kuma nuna cewa, kashi 57 na mace-macen ya faru ne a jihohi 5 na arewacin Nijeriya, a inda Jihar Benuwai ke a kan gaba da mutuwar mutum 120, Jihar Kaduna na biye da mutuwar mutum 69 sai kuma JIhar Zamfara inda mutum 60 suka mutu sai Jihar Filato inda mutum 48 suka mutu haka kuma mutum 42 sun mutu a Jihar Neja a daidai lokacin da muke magana a kai. Jihohin da aka samu mace-mace sun kuma hada da Abia, Osun, Ekiti da inda mutum dai-dai suka mutun sai Jihar Bayelsa inda mutum 2 suka mutu, Jihar Kano kuma mutum 3, haka kuma a jihohin Nasarawa, Ribers, Gombe da Ondo an rasa rayukan mutum 4 a kowannensu.
Bayanai daga kididdigar jaridar Daily Trust na wadanda aka sace ya nuna cewa, daga cikin mutum 1,321 da aka sace a tsakanin watan Satumba zuwa Disamba ya nuna cewa kashi 84 na wadanda aka sacen sun fito ne daga arewacin Nijeriya, inda kashi 16 kuma aka sace su a kudancin kasar. Haka kuma bayanin ya nuna cewa, kashi 62 na sace-sacen mutane da aka yi an yi ne a jihohi 5 na arewacin Nijeriya wadanda suka hada da Jihar Kaduna, Zamfara, Nija, Katsina da Sakkwato. Jihar Kaduna ne a kan gaba da mutum 256 sai Jihar Zamfara inda aka sace mutum 246 a Jihar Neja an sace mutum 127 a Jihar Katsina an sace mutum 116 yayin da kuma aka sace mutum 74 a Jihar sakkwato.
Bayanin ya nuna cewa, mutum dai-dai aka sace a Jihohin Osun da Legas inda kuma aka samu labarain sace mutum biyu-biyu a jihohin Kano, Gombe da Abia, yayin da aka samu rahoton sace mutum uku a JIhar Jigawa inda kuma aka sace mutum biyu a Jihar Bauchi an kuma sace mutum biyar a Jihar Imo.
Kididdigar ya nuna raguwar da aka samu a yawan mace-mace musamman a Jihar Kaduna inda a baya (watan Afrilu zuwa Yuni) mutum 285 suka mutu a tsakianin watan yuli zuwa Satumba kuma mutun 161 ne suka mutu.

•Kudu Maso Gabashin Nijerriya Aka Fi Kashe ‘Yansanda
A kudu maso gabashin Nijeriya inda ‘yan kungiyar IPOB suka zafafa hare-hare a kan cibiyoyn jami’an tsaro, sun samu nasarar kashe jami’an tsaro 24 a jihohin Inugu, Imo, Anambra, Ebonyi da Abia a tsakanin watan Satumba zuwa Disamba. Sai yankin Arrewa maso Yamma inda ayyukan ‘yan ta’adda ya yi sanadiyyar mutuwar jami’an ‘yansanda 9 a jihohn Kebbi, Sokoto, Katsina da kuma Kaduna. Rundunar ‘yansanda ta kuma rasa jami’ai 7 a yankin kudu maso kudancin kasar a jihohin Ribers da Edo an kuma kashe ‘yansanda 4 a arewa ta tsakiya inda jihohin Benuwai, Kogi da yankin Abuja. Haka kuma ‘yansanda 3 sun mutu a yankin kudu maso yammacin kasar nan na jihohin Ekiti da Oyo. Amma kuma duk da harkokin ta’addanci a yankin arewa maso gabas babu rahoton kashe jami’in ‘yansanda a yankin, sai dai an samu rahoton kashe sojoji 10 a Jihar Borno.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

•An Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama A Cikin Wata 4
Duk da rashin iya kawo karshen kashe-kashe a Nijeriya da juami’an tsaro suka kasa sun samu gaggarumar nasara tun bayan da Shugaban Kasa Buhari ya bayar da umarnin a kawo karshen harkokin ta’addanci zuwa karshen watan Disamba na shekarar 2022.
Kididdiga ya nuna cewa, jami’an tsaron Nijeriya sun kashe ‘yan ta’adda 267 a Jihar Borno a tsakanin watan Satumba zuwa Disamba. Haka kuma an kashe fiye da ‘yan ta’adda 200 a hare-haren jiragen sama dana sojojin kasa a yankin Jihar Zamfara ta tsakiyar watan Nuwamba.
Haka kuma an kashe wasu ‘yan ta’adda 34 a yankin Jihar Kaduna kamar dai yadda kwamishinan kula da tsaron cikin gida Mista Samuel Aruwan ya sanar.
Bincike ya nuna cewa, wadanda aka kashen zai iya zarce wadannan alkaluma musamman ganin sau da yawa jami’an tsaro na tabbatar da kashe ‘yan ta’adda da dama amma ba tare da bayar da kididdigar yawan wadanda aka kashen ba.

•Masana Sun Ce Al’amarin Tsaro Ya Inganta
Duk da yawan alkaluman kashe-kashe da garkuwa da mutane da aka yi a cikin watanni hudu, masana a bangaren harkar tsaraon sun nuna cewa, an samu ingantuwar harkar tsaro tun bayan da Shugaba Buhari ya bayar da umarnin a kawo karshen ayyukan ta’addanci zuwa watan Disamba. “Ba zai taba yiwuwa ba a kawar da harkokin ta’addanci gaba daya ba” in ji Dakta Tanko masani a harkar tsaro a makarantar yaki ta ‘War College’ da ke Abuja.
“A yankin Arewa maso Gabas al’umma na ta komawa gidajensu bayan hijirar da suka yi, in har babu ingantuwa tsaro ta yaya za su koma?, akwai kuma bukatar jami’an tsaro su hada hannun tare da aiki da al’umma don samun cikakken nasarar da ake buikata.
“Tabbas an samu raguwar hare-haren ‘yan Boko Haram, da yawa daga cikin su suna ta mika wuya, an kuma samu cikakken tsaro a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja. ‘Yan Nijeriya na zirga-zirgar su a halin yanzu cikin aminc,” in ji shi.
Wani tsohon mataimaikin shugaban rundunar ‘yansandan Nijeriya, (AIG), Wilson Inalegwu ya tabbatar da samu ingantuwar lamarin tsaro a Nijeriya, “Al’umma da dama na iya tafiye-tafiye a ba tare da wani tsoro ba kamar yadda ake yi a can da, an samu karuwar tsaro a kan hanyoyinmu.”
Inalegwu wanda tsohon kwamishinan ‘yansandan Abuja ne ya kuma nuna takaicinsa a kan yadsda ake samun karuwar hare-hare a kan jami’an tsaro musamman a kan ‘yansanda a yankin kudu masu gabashn kasar nan.”
“A tunani na harkokin IPOB dana ‘Eastern Security Network’ irin na ‘yan tawaye ga gwamnatin tarayya ne shi ya sa suke ganin juami’an tsaro musamman ‘yansanda a matsayin abokan gaba,” in ji shi.

•Masana Sun Nemi A Bayar Da Karfi A Kan Neman Bayanan Sirri Daga Al’umma
Dukkan su, Dakta Ahmed da AIG Inalegwu (Mai ritaya), sun bayyana cewa, in har ana son a kawo karshen manyan matsalolin tsaron kasar nan dole a sauya fasalin tsarin jami’an tsaronmu, daga tsarin da aka san shi a da zuwa yadda za a yi aiki tare da al’umma don hada hannu a kawo kaeshen matsalar tsaro a kasar baki daya.
“Inda nine shugaban kasa ba zan sake ba jami’an tsaro wani wa’adi ba kuma amma zan dai basu dukkan tallafin da suke bukata na ganin an samar da tsaro a Nijeriya zan kuma yi amfani da dukkan hukumomin gwamnati don su zaburantar da al’umma wajen bayar da gudunmawar ganin suna bayar da bayanan sirri ga jami’an tsaro don su samu nasarar murkushe harkokin ‘yan ta’adda gaba daya,” in ji Dakta Tanko Ahmed.
Shi kuwa AIG Wilson Inalegwu (Mai Ritaya), ya bayyana cewa, za a iya cimma gaggarumn nasara a yaki da ta’addanci ta hanyar amfani da da bayanan sirri daga al’umma tare da kuma yin kuste a cikin ‘yan ta’addan ta yadda za a rika sanin halin da suke ciki a lokacin da suke shiryawa da kuma tattauna yadda za su kai hari tun kafin su kai harin.

•Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Gum A Kan Wa’adin Da Ta Bayar
A halin yanzu kuma fadar shugaban kasa ta ki cewa komai a kan wa’adin da ta ba jami’an tsaro na su kawo karshen harkokin ta’addanci a Nijeriya zuwa ranar 31 ga watan Disamba 2022.
Mataimakin shugaban kasa na musamman na kan harkokin yada labarai, Malam Garba Shehu, bai amsa sakon da aka yi masa ba bayan da ka yi ta kiran wayarsa a daidai lokacin da ake shirya wannan rahoton.
Amma kuma idan za a iya tunawa a jawabinsa na shiga sabuwar shekarar 2023, shugaban kasa ya bayyana cewa, gwamnatinsaa za ta samar da sabbin tsare-tsare wadanda za su kai ga kawo karshen mastalar tsaro da bunkasar tattalin arzikin kasa tare da kuma yaki da cin hanci a dukkan bangarorin gwamnati.
Shugaban kasan ya ce, yakin da ake yi da masu garkuwa da mutane da sauran ayyukin ta’addanci a yankin arewa maso yamma na samun nasara sosai, ya kuma bayar da misali da dawowar harkokin zirga-zirgar jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja.
Ya kuma kara da cewa, an samu gaggarumin nasara a fattakar ‘yan ta’adda a yankin arewa maso gabas, wanda hakan ke nuna nasarar da ake samu a yankin gaba daya a wannan shekarar.
“Zamu ci gaba da fattakarsu da tarwatsa harkokin ‘yan ta’adda a dukkan sassan Nijeriya tare da aiki da al’umnma domin samun cikakiyyar nasara a kan ‘yan ta’adda don sai an hada hannun da mutane gaba daya,” in ji shugaban kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Dakatar Da Karuwar Hare-hare A Kan Likitoci – Ra’ayinmu

Next Post

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

6 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

7 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

8 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

12 hours ago
tsaro
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

13 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

14 hours ago
Next Post
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.