• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Tsaro Da Ambaliya: ‘Yan Nijeriya Sun Sayo Abinci Daga Waje Na Tiriliyan 3 – CBN

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
tallafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bayyana cewa ‘yan Nijeriy sun kashe dalar Amurka biliyan 2.13 wajen shigo da kayan abinci daga kasashen ketare a shekarar 2023.

A cewar rahoton kiddiga na zanga-zango da CBN ya fitar, akwai bukatu da dama da kasashen waje ke da su kan Afrika duk da cewa nahiyar na matukar fifita sayo kayan abinci daga can.

  • Jami’ai Sun Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Karkashin Dandalin FOCAC 
  • Za A Fara Rabon Takin CBN Kyauta, Sai Dai Masana Sun Ba Da Shawara

Wannan dai na zuwa ne a yayin da farashin kayayyakin abinci da ake shigo da su cikin Nijeriya ya karu zuwa babban mataki, inda ya kai har zuwa kaso 34 cikin 100 a cikin shekara guda tsakanin watan Afrilun 2023 zuwa Afrilun 2024.

Farashin kayan abinci dai ya yi tashin gwauron zabi a nahiyar Afrika sakamakon lamuran da suka shafi harkokin duniya, inda nahiyar ke kan gaba-gaba wajen shigo da kayayyaki a kasashen waje domin amfanin kai da kai.

Makuden kudaden da ake kashewa wajen sayo kayan abinci a kasashen waje na daga cikin manyan damuwowin da ke shafan tattalin arzikin Nijeriya. Kasar tana da dubban albarkatun gona, kuma akwai sa’ayin da ake ta kan yi wajen fitar da abincin gida duk a kokarin ganin an rage dogaro da shigo da kayan abinci a kasashen waje.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Sai dai, matsalolin da suka shafi na rashin kyan hanyoyi, matsalar tsaro, canjin yanayi su na taka rawa wajen dakile manufar da aka sanya a gaba na dogara da abincin gida.

Gwamnatin tarayya ta taba yin fatali da shigo da kayayyakin abinci na kasashen waje a wani matakin magance tsadar kayan abinci da kuma matsin rayuwa da al’umma suka shiga.

Tulin kudin da aka kashe wajen sayo kayan abincin kamar yadda masana suka ce, kai tsaye na nuni da cewa gwamnatin Nijeriya har yanzu ba ta dauki matakin magance matsalar yunwa da fatara zuwa shekarar 2030 ba, kamar yadda ke kunshe cikin shirin cimma muradin karni na majalisar dinkin duniya.

A shekarar 2023 kamar yadda kiddigar ya nuna, an kashe dala miliyan 245.7 wajen shigo da kayan abinci a watan Janairu, dala miliyan 163.6 a watan Fabrairu, dala miliyan 268.4 a watan Maris, dala miliyan 240.9 a watan Afrilu, dala miliyan 238.3 a watan Mayu da kuma dala miliyan 206.1 aka rasa wajen sayo kayan abinci a watan Yuni.

A watan Yuli na 2023 kuwa, babban bankin kasar nan ya ce an fitar da kudin da ya kai dala miliyan 58 wajen sayo kayan abinci kawai, dala miliyan 95.3 a watan Agusta, dala miliyan 119.9 a Satumba, dala miliyan 132.4 a Oktoba, dala miliyan 235.9 a Nuwamba da kuma dala miliyan 126.2 a watan Disamban bara.

A watan Afrilun 2024, rahoton hauhawar farashin kayan abinci da hukumar kidddiga ta kasa (NBS) ta fitr, ya karu daga kaso 15.92 cikin dari zuwa 40.53, sakamakon tashin farashin fulawa, garri, buredi, alkama, semolina, doya, mangyade, kifi, nama, hatta, kaji, mango, ayaba, kayan marmari na lambu, lipton na shayi, bombita, miliya, madara, da dai sauran nau’ikan kayan abinci.

Da yake tofa albarkacin baki kan wannan lamarin, shugaban kungiyar manoma a Nijeriya, Kabir Ibrahim, ya ce a halin da ake ciki duk da wannan adadin kudin da aka kashe wajen shigo da kayayyakin, ba wai an amincewa da a shigo da kowani irin kaya ba ne.

Ya ce, tabbas za a iya samun karuwar adadin a wannan shekarar sakamakon kara dogara da ake yi wajen sayo kayan abinci daga kasashen waje.

Kabir ya nuna cewa a shekarun da aka hana shigo da kayan abinci daga kasashen waje ba a kashe wadannan makuden kudaden ba, amma yanzu an dauko hanyar ci gaba da salwatar da makuden kudade domin shigo da kayan abincin kasashen waje.

Ya nuna cewa idan da za a maida hankali kan kayan abicin da ake nomawa a cikin gida, zai kawo karshen matsaloli da dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CBNlamunin BankiNomaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rundunar Sojojin Kasar Sin Ta Ci Gaba Da Yin Atisayen Soja a Wuraren Dake Kewayen Tsibirin Taiwan

Next Post

An Bude Taron Koli Karo Na 7 Na Raya Yanar Gizo Na Sin 

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

21 minutes ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

3 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya
Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

4 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

5 hours ago
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

17 hours ago
Next Post
An Bude Taron Koli Karo Na 7 Na Raya Yanar Gizo Na Sin 

An Bude Taron Koli Karo Na 7 Na Raya Yanar Gizo Na Sin 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.