ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Fara Rabon Takin CBN Kyauta, Sai Dai Masana Sun Ba Da Shawara

by Abubakar Abba
2 years ago
Takin

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci ta Tarayya, ta shirya tsaf; domin fara rabon buhunan takin zamani miliyan 2.15, wanda Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya ba ta kauta.

Wasu masana a fannin aikin noma a kasar nan; sun bayar da shawarar cewa, duba da yadda aka fara samun ruwan sama a wasu sassan yankunan kasar nan, ya kamata a fara raba wa manoma takin a kan lokaci, musamman domin samar da wadataccen abinci.

  • Sin Ta Bukaci Philippines Da Ta Dakatar Da Tada Zaune Tsaye A Yankin Tekun Kudancin Sin
  • Ziyarar Xi Jinping A Turai Ta Fitar Da Muryar Kiyaye Zaman Lafiya Da Yin Hadin Gwiwa

Sai dai, wata majiya a ma’aikatar ta bayyana cewa, an samu jinkirin rabar da takin zamanin ne; sakamakon gudanar da binciken da aka yi na zargin cewa, takin ya lalace.

A cewar majiyar, “Babban Bankin CBN, ba wani sabon takin zamanin zai sayo ba, sauran wanda Tsohon Gwamnan Babban Bankin, Godwin Emefiele ya gaza rabawa ne a karkashin shirin  aikin noma na babban bankin, wato ‘Anchor Borrower Programme’.”

Har ila yau, majiyar ta kara da cewa; wannan taki, bankin CBN ne ya mika wa ma’aiktar aikin noma, amma akwai wasu abubuwa da ma’aikatar ke bukatar tantacewa kafin ta fara rabar da takin.

Haka kazalika, akwai wani zargi da ake yi na cewa, tuni takin ya jima da lalacewa.

Koda-yake, an kuma ruwaito cewa; Daraktan sashen kula da ayyukan samar da kayan aiki noma na ma’aikatar, Abana Waziri Abba, ya karyata batun zargin lalacewar takin zamanin.

Sai dai kuma, ya aminta da cewa; sashen ya dauki samfurin takin, don gudanar da gwaji a dakunan gwaje-gwajen da ake da su a Jihar Kaduna da Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya da kuma Jami’ar  Bayero da ke Kano, don tabbatar da ingancinsa; domin wannan sashe ne ke da alhakin tabbatar da ingancin kowane irin taki a fadin kasar nan.

A cewarsa, sakamakon binciken ya nuna cewa, takin na da inganci; sannan kuma za a iya sayar wa da manoma, inda ya sanar da cewa, sai dai kawai wasu ‘yan matsaloli da ba za a rasa ba a kan takin.

Sai dai, bai yi bayani dalla-dalla kan yadda za a yi rabon takin ga manoman da ke fadin Nijeriya ba.

Kazalika, yawan takin ya kai kimanin buhu miliyan 2.15, sannan kowane nauyin buhu daya ya kai nauyin kilo 50.

Sa’annan, nau’in takin ya hada da NPK tan 27,250; 20-10-10 da wani tan 27,110.00 na NPK 27-13-13 da tan 18,904.55 na NPK 15-15-15  378,091 da tan  31,772.18 na nau’in UREA 635,444 da kuma tan 2,500 na nau’in  SSP 50,000.

Jimillar wadannan nau’ikan baki-daya ya kai yawan buhu 2,150,735, wadanda awonsu ya kai kimanin tan 107,536.73.

Takin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Tsohon Firaministan Faransa: Duniya Na Hasashen Kyakkyawar Makoma Ga Kasar Sin

Tsohon Firaministan Faransa: Duniya Na Hasashen Kyakkyawar Makoma Ga Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.