ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Fara Rabon Takin CBN Kyauta, Sai Dai Masana Sun Ba Da Shawara

by Abubakar Abba
2 years ago
Takin

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci ta Tarayya, ta shirya tsaf; domin fara rabon buhunan takin zamani miliyan 2.15, wanda Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya ba ta kauta.

Wasu masana a fannin aikin noma a kasar nan; sun bayar da shawarar cewa, duba da yadda aka fara samun ruwan sama a wasu sassan yankunan kasar nan, ya kamata a fara raba wa manoma takin a kan lokaci, musamman domin samar da wadataccen abinci.

  • Sin Ta Bukaci Philippines Da Ta Dakatar Da Tada Zaune Tsaye A Yankin Tekun Kudancin Sin
  • Ziyarar Xi Jinping A Turai Ta Fitar Da Muryar Kiyaye Zaman Lafiya Da Yin Hadin Gwiwa

Sai dai, wata majiya a ma’aikatar ta bayyana cewa, an samu jinkirin rabar da takin zamanin ne; sakamakon gudanar da binciken da aka yi na zargin cewa, takin ya lalace.

A cewar majiyar, “Babban Bankin CBN, ba wani sabon takin zamanin zai sayo ba, sauran wanda Tsohon Gwamnan Babban Bankin, Godwin Emefiele ya gaza rabawa ne a karkashin shirin  aikin noma na babban bankin, wato ‘Anchor Borrower Programme’.”

Har ila yau, majiyar ta kara da cewa; wannan taki, bankin CBN ne ya mika wa ma’aiktar aikin noma, amma akwai wasu abubuwa da ma’aikatar ke bukatar tantacewa kafin ta fara rabar da takin.

Haka kazalika, akwai wani zargi da ake yi na cewa, tuni takin ya jima da lalacewa.

Koda-yake, an kuma ruwaito cewa; Daraktan sashen kula da ayyukan samar da kayan aiki noma na ma’aikatar, Abana Waziri Abba, ya karyata batun zargin lalacewar takin zamanin.

Sai dai kuma, ya aminta da cewa; sashen ya dauki samfurin takin, don gudanar da gwaji a dakunan gwaje-gwajen da ake da su a Jihar Kaduna da Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya da kuma Jami’ar  Bayero da ke Kano, don tabbatar da ingancinsa; domin wannan sashe ne ke da alhakin tabbatar da ingancin kowane irin taki a fadin kasar nan.

A cewarsa, sakamakon binciken ya nuna cewa, takin na da inganci; sannan kuma za a iya sayar wa da manoma, inda ya sanar da cewa, sai dai kawai wasu ‘yan matsaloli da ba za a rasa ba a kan takin.

Sai dai, bai yi bayani dalla-dalla kan yadda za a yi rabon takin ga manoman da ke fadin Nijeriya ba.

Kazalika, yawan takin ya kai kimanin buhu miliyan 2.15, sannan kowane nauyin buhu daya ya kai nauyin kilo 50.

Sa’annan, nau’in takin ya hada da NPK tan 27,250; 20-10-10 da wani tan 27,110.00 na NPK 27-13-13 da tan 18,904.55 na NPK 15-15-15  378,091 da tan  31,772.18 na nau’in UREA 635,444 da kuma tan 2,500 na nau’in  SSP 50,000.

Jimillar wadannan nau’ikan baki-daya ya kai yawan buhu 2,150,735, wadanda awonsu ya kai kimanin tan 107,536.73.

Takin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Tsohon Firaministan Faransa: Duniya Na Hasashen Kyakkyawar Makoma Ga Kasar Sin

Tsohon Firaministan Faransa: Duniya Na Hasashen Kyakkyawar Makoma Ga Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.