• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Tsaro Da Ambaliya: ‘Yan Nijeriya Sun Sayo Abinci Daga Waje Na Tiriliyan 3 – CBN

byKhalid Idris Doya
1 year ago
tallafi

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bayyana cewa ‘yan Nijeriy sun kashe dalar Amurka biliyan 2.13 wajen shigo da kayan abinci daga kasashen ketare a shekarar 2023.

A cewar rahoton kiddiga na zanga-zango da CBN ya fitar, akwai bukatu da dama da kasashen waje ke da su kan Afrika duk da cewa nahiyar na matukar fifita sayo kayan abinci daga can.

  • Jami’ai Sun Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Karkashin Dandalin FOCAC 
  • Za A Fara Rabon Takin CBN Kyauta, Sai Dai Masana Sun Ba Da Shawara

Wannan dai na zuwa ne a yayin da farashin kayayyakin abinci da ake shigo da su cikin Nijeriya ya karu zuwa babban mataki, inda ya kai har zuwa kaso 34 cikin 100 a cikin shekara guda tsakanin watan Afrilun 2023 zuwa Afrilun 2024.

Farashin kayan abinci dai ya yi tashin gwauron zabi a nahiyar Afrika sakamakon lamuran da suka shafi harkokin duniya, inda nahiyar ke kan gaba-gaba wajen shigo da kayayyaki a kasashen waje domin amfanin kai da kai.

Makuden kudaden da ake kashewa wajen sayo kayan abinci a kasashen waje na daga cikin manyan damuwowin da ke shafan tattalin arzikin Nijeriya. Kasar tana da dubban albarkatun gona, kuma akwai sa’ayin da ake ta kan yi wajen fitar da abincin gida duk a kokarin ganin an rage dogaro da shigo da kayan abinci a kasashen waje.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Sai dai, matsalolin da suka shafi na rashin kyan hanyoyi, matsalar tsaro, canjin yanayi su na taka rawa wajen dakile manufar da aka sanya a gaba na dogara da abincin gida.

Gwamnatin tarayya ta taba yin fatali da shigo da kayayyakin abinci na kasashen waje a wani matakin magance tsadar kayan abinci da kuma matsin rayuwa da al’umma suka shiga.

Tulin kudin da aka kashe wajen sayo kayan abincin kamar yadda masana suka ce, kai tsaye na nuni da cewa gwamnatin Nijeriya har yanzu ba ta dauki matakin magance matsalar yunwa da fatara zuwa shekarar 2030 ba, kamar yadda ke kunshe cikin shirin cimma muradin karni na majalisar dinkin duniya.

A shekarar 2023 kamar yadda kiddigar ya nuna, an kashe dala miliyan 245.7 wajen shigo da kayan abinci a watan Janairu, dala miliyan 163.6 a watan Fabrairu, dala miliyan 268.4 a watan Maris, dala miliyan 240.9 a watan Afrilu, dala miliyan 238.3 a watan Mayu da kuma dala miliyan 206.1 aka rasa wajen sayo kayan abinci a watan Yuni.

A watan Yuli na 2023 kuwa, babban bankin kasar nan ya ce an fitar da kudin da ya kai dala miliyan 58 wajen sayo kayan abinci kawai, dala miliyan 95.3 a watan Agusta, dala miliyan 119.9 a Satumba, dala miliyan 132.4 a Oktoba, dala miliyan 235.9 a Nuwamba da kuma dala miliyan 126.2 a watan Disamban bara.

A watan Afrilun 2024, rahoton hauhawar farashin kayan abinci da hukumar kidddiga ta kasa (NBS) ta fitr, ya karu daga kaso 15.92 cikin dari zuwa 40.53, sakamakon tashin farashin fulawa, garri, buredi, alkama, semolina, doya, mangyade, kifi, nama, hatta, kaji, mango, ayaba, kayan marmari na lambu, lipton na shayi, bombita, miliya, madara, da dai sauran nau’ikan kayan abinci.

Da yake tofa albarkacin baki kan wannan lamarin, shugaban kungiyar manoma a Nijeriya, Kabir Ibrahim, ya ce a halin da ake ciki duk da wannan adadin kudin da aka kashe wajen shigo da kayayyakin, ba wai an amincewa da a shigo da kowani irin kaya ba ne.

Ya ce, tabbas za a iya samun karuwar adadin a wannan shekarar sakamakon kara dogara da ake yi wajen sayo kayan abinci daga kasashen waje.

Kabir ya nuna cewa a shekarun da aka hana shigo da kayan abinci daga kasashen waje ba a kashe wadannan makuden kudaden ba, amma yanzu an dauko hanyar ci gaba da salwatar da makuden kudade domin shigo da kayan abincin kasashen waje.

Ya nuna cewa idan da za a maida hankali kan kayan abicin da ake nomawa a cikin gida, zai kawo karshen matsaloli da dama.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
An Bude Taron Koli Karo Na 7 Na Raya Yanar Gizo Na Sin 

An Bude Taron Koli Karo Na 7 Na Raya Yanar Gizo Na Sin 

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version