• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mauludi: Buhari Ya Bukaci ’Yan Siyasa Su Guje Wa Amfani Da Kalaman Batanci

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Mauludi: Buhari Ya Bukaci ’Yan Siyasa Su Guje Wa Amfani Da Kalaman Batanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bukaci ‘yan siyasa a wannan kakar zabe da su guji yin amfani da kalaman batanci. 

A sakonsa na fatan alheri ga al’ummar Musulmi a wajen Mauludi na murnar zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAW), Shugaban ya kuma bukaci ‘yan siyasa da su kaucewa wulakanci da wulakanta abokan hamayya.

  • 2023: Matasa A Kano Sun Yi Alkawarin Yi Wa ‘Yan Siyasa Masu Ingiza Su Shaye-shaye Tutsu -Fatima Jikan Dan’uwa
  • Kasar Sin Ta Mika Dakin Adana Magunguna Na Zamani Ga Zimbabwe

Shugaban kasar a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Garba Shehu, ya fitar a ranar Juma’a, ya sake yin alkawarin cewa zai tabbatar da sahihin zabe da gaskiya a 2023.

Ya kuma bukaci al’ummar musulmi da su yi koyi da kyawawan dabi’u na Annabi Muhammad (SAW) inda ya ce “mafificiyar hanyar girmamawa shi ita ce koyi da kyawawan halayen Fiyayyen Halitta”.

Buhari ya bayyana cewa “Annabi ya shahara da tawali’u da kuma adalci.”

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

A cewar shugaba Buhari, “Manzon Allah ya jawo hankalin mutane zuwa ga addinin musulunci ta hanyar gaskiya da rikon amana da adalci da hakuri da juriya”.

Ya bayyana cewa Annabi ya yi rayuwa ta hakuri a karkashin girmama yarjejeniyar wadanda ba musulmi ba domin zaman lafiya.”

Shugaba Buhari ya kara da cewa “Gaskiya na daya daga cikin manya-manyan dabi’un Manzon Allah SAW kuma duk musulmin kirki ya yi koyi da shi.”

Shugaban ya yi amfani da wannan damar wajen yin kira ga ‘yan Nijeriya da su ba gwamnati hadin kai a kokarin da ake yi na kawar da rashin tsaro da cin hanci da rashawa; su kara girmama mata da yara da masu karamin karfi; da kuma nuna kauna da fahimtar juna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariFiyayyen HalittaHakuriHalaye Na GariManzon Allah SAWMaulidi
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Matasa A Kano Sun Yi Alkawarin Yi Wa ‘Yan Siyasa Masu Ingiza Su Shaye-shaye Tutsu -Fatima Jikan Dan’uwa

Next Post

2023: Ko Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Tsakanin‘Yan Takara Za Ta Haifar Da Da Mai Ido?

Related

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

3 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

4 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

6 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

7 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

8 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

13 hours ago
Next Post
2023: Ko Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Tsakanin‘Yan Takara Za Ta Haifar Da Da Mai Ido?

2023: Ko Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Tsakanin‘Yan Takara Za Ta Haifar Da Da Mai Ido?

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.