ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Matasa A Kano Sun Yi Alkawarin Yi Wa ‘Yan Siyasa Masu Ingiza Su Shaye-shaye Tutsu -Fatima Jikan Dan’uwa

by Abdullahi Muh'd Sheka
4 years ago
'Yan Siyasa

28 ga watan Satumbar da ya gabata ne Hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa ta ayyana sakin takunkumin fara yakin neman zaben Shekara ta 2023, wanda hakan ke nuni da cewa kakar zaben ta kankama.

Akan haka Gidauniyar da ke yaki da Shan Miyagun Kwayoyi ta Kasa YADAF Karkashin Jagorancin Shugabar Gidauniyar Hajiya Fatima Bature Jikan Dan-Uwa ta bayyana fito da wasu tsare tsaren domin dakile al’adar wasu ‘yan siyasa dake durawa matasa Kayan maye domin biyan bukatun kansu.

  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Tsoho Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Har Abada Kan Laifin Fyade A Jigawa
  • Kotun Daukaka Kara Ta Umurci Kungiyar ASUU Da Ta Gaggauta Janye Yajin Aikin Da Take

Hajiya Fatima Bature JikanDan-Uwa ta bayyana Haka ne a lokacin kaddamar zagayen matattaran masu sayarwa tare ta Shan Miyagun Kwayoyi a Kano, Shirin Wanda shi ne irin sa na farko da wata kungiya ke tattalin kafa da kafa har matattarar matasa inda ake tattaunawa da su Kan dalilan da Suka jefa su cikin wannan mummunar ta’ada.

ADVERTISEMENT

Ya ce jama’a kowa zai yi mamakin Jin dalilan wasu yaran na hakura da harkar Karatu sun gwammace afkawa cikin wannan harka ta shaye shaye.

“Wani abin mamaki da yawayaran da Gidauniyar YADAF tazanta dasu alokacin data Fara wannan zagayen kwakwaf, sun bayyana cewa Matsalar Jarrabawar Kualify ce sanadiyyar fadawa harkar Shaye-Shaye, a cewar yaran yaro yaci credit 8 Amma Gwamnati ya ce ba zata biya Masa tallafin kudin Jarrabawar ba sai abin da ya Kama daga credit 9 zuwa sama, sannan ga halin matsin tattalin arziki da ake fama dashi a kasa baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

Wannan ta sa iyaye basa iya kashe wadannan makudan kudade domin biya wa yaransu Jarrabawar.

Saboda haka dole zaman Gida ya kama su,Kuma akan Haka sai ake gamuwada wasu da suka Jima a cikin harkar suna ba su shawarar Shan abinda zai rage masu wannan radadi daga nan Suka tsinci kansu a irin wannan Hali.

Hajiya Fatima Bature Jikan Dan-Uwa ta ci gaba cewa zuwa yanzu da muke wannan zagayen matattaran matasa mun sama da matasa 70 da Suka Kawo kansu domin Mayar da su makarantunsu, wannan Gidauniya ta Mayar da su tare da biya masu kudaden Jarrabawar, yanzu Haka akwai sansanin guda da tuni ya tashimatasan duk mun Mayar da su Makarantu. Ya ce  wannan na nuni da cewa zaben Shekara 2023 a Kano Babu matasa masu shaye-shaye a cikinsa, kowa ya Koma makaranta sauran Kuma tuni mun kammala Shirin bude cibiyar koyar da sana’o’i domin matasa su samu sana’ar dogaro da Kai maimakon bin ‘yan siyasar da su’ya’yansu na tura suna Karatun,mu Kuma an bar yaranmu ana takashe su ba gaira ba dalili.

Domin tabbatar da hadin guiwa da Hukumomin tsaro, Muna tunawa Hukumar zaben dokar da Gwamnati ta samar na tabbatar da gwajin kwakwalwar duk wani Mai bukatar yin takara domin tabbatar ba ya mu’amala da Miyagun Kwayoyi, ta ce a wannan gaba dole a jinjinawa Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, wanda shi tun a zabukan baya ya fara gwada wannan doka inda aka tabbatar da Sai da aka tura duk wani dan takara a Kano Hukumar da ke yaki da sha tare da fataucin Miyagun Kwayoyi NDLEA, inda aka tantace ‘yan takarkarun, har ma aka dakatar da wasu da aka samu da Matsalar shaye-shaye a cikinsu.

Ya ce yanzu haka za mu yi amfani da matasa tare da duk mai kishin ci gaban Jihar Kano da kuma masu yi wa Kano da Kasa fatan alhairi, domin bibiyar duk wani dan takara da ya nuna rashin kulawa da wannan doka ta kaucewa raba wa matasa kwayan maye a lokacin yakin neman zabe, zamu kuma bayyanawa duniya abin da muka samu kan haka, sannan zamu hada hannuda Jami’an Hukumar NDLEA domin kwarmata duk wanda ya tanadi kayan maye domin gurbata hankulan matasa.

“Sashin mu na tattaunawa da masu irin wannan matsala sun bayyana mana yadda wasu ‘yan siyasa ke amfani da matasa ta hanyar basu kayan maye domin samun damar cin karensu babu babbaka, saboda haka tuni wasu daga cikin ire-iren wadannan matasa sun zubar da makamansu tare alkawarin yin aiki tare da wannan Gidauniya domin ganin ba a yi amfani da matasan ba Wajen badakala a lokacin yakin neman zabe da ma lokacin Zaben ba.

Hajiya Fatima ta bayyana nasarar da wannan Gidauniyata samu daga lokacin kafuwarta zuwa yau, ta ce mun samu nasarar ziyartar Sarakuna, manyan attajirai, Jami’an Gwamnati, Malamai da limamai domin ganinmun hada hannu wajen yakar wannan babbar matsàla.

Wanda zuwa yanzu muna kara yiwa Allah godiya domin kwalliya na biyan kudin sabulu. Daga nan sai Hajiya Fatima Bature Jikan Dan-Uwa tayi amfani da wannan dama Wajen jan hankalin iyaye wajen lura da mutanen da yaransu ke mu’amala da su, domin abokai na taka muhimmiyar rawa wajen lalata rayuwar matasan wannan lokaci.

Haka ita ma tsangwama, rabuwar iyali, talauci da Matsalar rayuwar zaman aure na cikin abubuwan da ke jefa wasu matasan cikin wannan mummunan ta’ada.

A karshe Hajiya Fatima Bature ta bukaci hadin kan iyaye, Malamai, Sarakuna, Gwamnatoci da dukkan masu ruwa da tsaki domin hada hannu wajen tunkarar wannan matsala.

'Yan Siyasa
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai
Rahotonni

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Noma
Rahotonni

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Next Post
Mauludi: Buhari Ya Bukaci ’Yan Siyasa Su Guje Wa Amfani Da Kalaman Batanci

Mauludi: Buhari Ya Bukaci ’Yan Siyasa Su Guje Wa Amfani Da Kalaman Batanci

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.