• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

MDD Da Gwamnatocin Kasashe Daban-Daban Sun Sake Jaddada Tsayawa Ga Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
MDD Da Gwamnatocin Kasashe Daban-Daban Sun Sake Jaddada Tsayawa Ga Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan Majalisar Dinkin Duniya, da gwamntocin kasashe daban-daban, sun ci gaba da mayar da martaninsu, inda suka yi Allah wadai da ziyarar kakakin majalisar wakilan Amurka Nancy Pelosi a yankin Taiwan, suna masu nuna adawa ga Amurka, saboda goyon-bayanta ga masu yunkurin balle Taiwan daga kasar Sin, tare kuma da jaddada matsayinsu, na tsayawa ga manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya.

Babbar darektar ofishin MDD dake birnin Vienna, Ghada Fathi Waly, ta sake nanata cewa, ofishinta yana girmama kudurorin babban taron MDD, da tsayawa tsayin daka kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya.

  • Amurka Ce Ke Yi Wa Zaman Lafiya A Zirin Taiwan Barazana

A nasa bangaren, shugaban kasar Masar Abdel Fattah al-Sisi, ya yi jawabin cewa, kasarsa tana tsayawa haikan, kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, kuma a ganinsa, hakan zai taimaka ga shimfida zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya baki daya.

Shi ma firaministan janhuriyar Afirka ta Tsakiya, Felix Moloua, da ministar harkokin wajen kasar Sylvie Baipo Temon, duk sun jaddada goyon bayan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, da kira ga bangarori masu ruwa da tsaki, su mutunta alkawuran siyasa da aka yi tsakanin Sin da Amurka.

Sa’anan kuma, mataimakin shugaban kasar Equatorial Guinea, Teodoro Nguema Obiang Mangue, ya bayyana cewa, kasar tana marawa kasar Sin baya, saboda kokarin da take yi, na kiyaye mulkin kai, da cikakken yankunan kasa, tare kuma da bukatar wasu kasashe da su dakatar da yunkurinsu na lalata zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Ministan kula da harkokin gida na kasar Laberiya Nathaniel McGill, ya bayyana cewa, kasarsa ta riga ta ayyana doka kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, kana kasar ba ta yarda da duk wani yunkuri na sabawa hakan ba.

Shi kuwa Okello Oryem, karamin ministan kula da harkokin waje na kasar Uganda, cewa ya yi kasarsa, za ta ci gaba da tsayawa haikan, kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya.

A cewarsa, ya dace kasashen yammacin duniya, ciki har da Amurka, su dakatar da yin shisshigi cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, kana, Uganda tana goyon-bayan matakan da kasar Sin take dauka, domin tabbatar da mulkin kai, da kiyaye cikakken yankin kasar. (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Naira Miliyan 5 Nake Nema Don Fansar Mahaifiyata – Mace Mai Safarar Kwayoyi

Next Post

Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

Related

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

8 hours ago
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

9 hours ago
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

10 hours ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

11 hours ago
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

12 hours ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

14 hours ago
Next Post
Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

LABARAI MASU NASABA

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.