ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

MDD Da Gwamnatocin Kasashe Daban-Daban Sun Sake Jaddada Tsayawa Ga Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

by CMG Hausa
4 years ago
MDD

Kwanan nan Majalisar Dinkin Duniya, da gwamntocin kasashe daban-daban, sun ci gaba da mayar da martaninsu, inda suka yi Allah wadai da ziyarar kakakin majalisar wakilan Amurka Nancy Pelosi a yankin Taiwan, suna masu nuna adawa ga Amurka, saboda goyon-bayanta ga masu yunkurin balle Taiwan daga kasar Sin, tare kuma da jaddada matsayinsu, na tsayawa ga manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya.

Babbar darektar ofishin MDD dake birnin Vienna, Ghada Fathi Waly, ta sake nanata cewa, ofishinta yana girmama kudurorin babban taron MDD, da tsayawa tsayin daka kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya.

  • Amurka Ce Ke Yi Wa Zaman Lafiya A Zirin Taiwan Barazana

A nasa bangaren, shugaban kasar Masar Abdel Fattah al-Sisi, ya yi jawabin cewa, kasarsa tana tsayawa haikan, kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, kuma a ganinsa, hakan zai taimaka ga shimfida zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya baki daya.

ADVERTISEMENT

Shi ma firaministan janhuriyar Afirka ta Tsakiya, Felix Moloua, da ministar harkokin wajen kasar Sylvie Baipo Temon, duk sun jaddada goyon bayan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, da kira ga bangarori masu ruwa da tsaki, su mutunta alkawuran siyasa da aka yi tsakanin Sin da Amurka.

Sa’anan kuma, mataimakin shugaban kasar Equatorial Guinea, Teodoro Nguema Obiang Mangue, ya bayyana cewa, kasar tana marawa kasar Sin baya, saboda kokarin da take yi, na kiyaye mulkin kai, da cikakken yankunan kasa, tare kuma da bukatar wasu kasashe da su dakatar da yunkurinsu na lalata zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Ministan kula da harkokin gida na kasar Laberiya Nathaniel McGill, ya bayyana cewa, kasarsa ta riga ta ayyana doka kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, kana kasar ba ta yarda da duk wani yunkuri na sabawa hakan ba.

Shi kuwa Okello Oryem, karamin ministan kula da harkokin waje na kasar Uganda, cewa ya yi kasarsa, za ta ci gaba da tsayawa haikan, kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya.

A cewarsa, ya dace kasashen yammacin duniya, ciki har da Amurka, su dakatar da yin shisshigi cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, kana, Uganda tana goyon-bayan matakan da kasar Sin take dauka, domin tabbatar da mulkin kai, da kiyaye cikakken yankin kasar. (Murtala Zhang)

MDD
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Next Post
Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
MDD

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
MDD

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
MDD

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.