• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Duniya Ke Fatan Gani Daga Tattaunawar Shugabannin Sin Da Amurka?

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Duniya ta shirya tsaf, tare da dakon muhimmiyar ganawar da za a yi gobe Laraba tsakanin shugabannnin manyan kasashe mafiya karfin tattalin arziki biyu na duniya, wato Sin da Amurka, karo na farko bayan tattaunawar da suka yi a tsibirin Bali, yau shekara 1 da ta gabata.

Rikici tsakanin Sin da Amurka, abu ne dake da mummunan tasiri ga ilahirin kasashen duniya ba wai kasashen biyu kadai ba, don haka, mai da wuka kube da dakatar da takalar fada da Amurka ke yi a kai a kai da hada hannu da Sin wajen jan ragamar al’amuran duniya, zai haifar da kyakkyawan tasirin da zai shafi kowanne lungu da sako na duniya, tare da samar da zaman lafiyar da muke muradi.

  • Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Hada Hannu Domin Kyautata Dangantakarsu
  • Yajin Aiki: TCN Ya Musanta Rahoton Datse Wutar Lantarki A Fadin Nijeriya

Ziyarar manyan jami’an Amurka a Sin, da ma na Sin a Amurka, ta share fagen tattaunawar shugabannin biyu, don haka abun da dukkanmu ke fata shi ne, ganin an aiwatar da sakamakon tattaunawar a aikace ba wai a fatar baki ba, kasancewar Amurka ta saba yin amai tana lashewa. A ganina tabbas zuwa yanzu, ta ga yadda dabi’arta ke hana ruwa guda, ko a dangantakarta da Sin ko kuma a harkokin duniya.

Kamar yadda ta sha nanata cewa ba ta neman takara ko cacar baki da Sin, to za mu yi fatan ganin kyautatuwar dangantaka, inda za su hada hannu wajen taimamakeniya da tuntubar juna da kara hadin gwiwa don ganin ci gaban kasashen biyu ba wai kokarin dakile kasar Sin ba.

Za mu yi fatan ganin Amurka ta daina yada jita-jita dangane da kasar Sin, haka kuma ta daina tsoma baki cikin harkokinta na gida. Dabaru da matakn Sin, sun riga sun dace da yanayinta da muradun al’ummarta, don haka, bai kamata a nemi kakaba mata wani ra’ayi na daban ba.

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

Muna fatan ganin an hada hannu tare da kokarin samar da duniya mai makoma ta bai daya da jituwa da girmama juna tsakanin mabanbanta al’ummomi da matsakaiciyar wadata, ta yadda za a shimfida ingantacciyar wurin rayuwa ga zuri’o’in dake tafe.

Haka zalika, muna sa ran ganin an gudanar da tattaunawar lami lafiya kamar yadda aka tsara da samun kyawawan sakamako, tare da dawowar shugaban kasar Sin gida lami lafiya. (Faeza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 10, 2025
Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya
Daga Birnin Sin

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Next Post
Cmg

CMG Ya Kimtsa Don Watsa Labarai Game Da Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 10, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

October 10, 2025
peter

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.