ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Duniya Ke Fatan Gani Daga Tattaunawar Shugabannin Sin Da Amurka?

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

Duniya ta shirya tsaf, tare da dakon muhimmiyar ganawar da za a yi gobe Laraba tsakanin shugabannnin manyan kasashe mafiya karfin tattalin arziki biyu na duniya, wato Sin da Amurka, karo na farko bayan tattaunawar da suka yi a tsibirin Bali, yau shekara 1 da ta gabata.

Rikici tsakanin Sin da Amurka, abu ne dake da mummunan tasiri ga ilahirin kasashen duniya ba wai kasashen biyu kadai ba, don haka, mai da wuka kube da dakatar da takalar fada da Amurka ke yi a kai a kai da hada hannu da Sin wajen jan ragamar al’amuran duniya, zai haifar da kyakkyawan tasirin da zai shafi kowanne lungu da sako na duniya, tare da samar da zaman lafiyar da muke muradi.

  • Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Hada Hannu Domin Kyautata Dangantakarsu
  • Yajin Aiki: TCN Ya Musanta Rahoton Datse Wutar Lantarki A Fadin Nijeriya

Ziyarar manyan jami’an Amurka a Sin, da ma na Sin a Amurka, ta share fagen tattaunawar shugabannin biyu, don haka abun da dukkanmu ke fata shi ne, ganin an aiwatar da sakamakon tattaunawar a aikace ba wai a fatar baki ba, kasancewar Amurka ta saba yin amai tana lashewa. A ganina tabbas zuwa yanzu, ta ga yadda dabi’arta ke hana ruwa guda, ko a dangantakarta da Sin ko kuma a harkokin duniya.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda ta sha nanata cewa ba ta neman takara ko cacar baki da Sin, to za mu yi fatan ganin kyautatuwar dangantaka, inda za su hada hannu wajen taimamakeniya da tuntubar juna da kara hadin gwiwa don ganin ci gaban kasashen biyu ba wai kokarin dakile kasar Sin ba.

Za mu yi fatan ganin Amurka ta daina yada jita-jita dangane da kasar Sin, haka kuma ta daina tsoma baki cikin harkokinta na gida. Dabaru da matakn Sin, sun riga sun dace da yanayinta da muradun al’ummarta, don haka, bai kamata a nemi kakaba mata wani ra’ayi na daban ba.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Muna fatan ganin an hada hannu tare da kokarin samar da duniya mai makoma ta bai daya da jituwa da girmama juna tsakanin mabanbanta al’ummomi da matsakaiciyar wadata, ta yadda za a shimfida ingantacciyar wurin rayuwa ga zuri’o’in dake tafe.

Haka zalika, muna sa ran ganin an gudanar da tattaunawar lami lafiya kamar yadda aka tsara da samun kyawawan sakamako, tare da dawowar shugaban kasar Sin gida lami lafiya. (Faeza Mustapha)

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Cmg

CMG Ya Kimtsa Don Watsa Labarai Game Da Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.