• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ke Jawo Hankalin Kamfanonin Kasa Da Kasa Zuwa Sin?

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

A baya bayan nan, manyan kamfanonin kasa da kasa suna kara shigowa kasar Sin domin gudanar da hada-hadar kasuwanci, da kaddamar da sabbin hajoji, da gudanar da baje koli da dai sauransu. Kamfanonin waje na da yakinin cewa, akwai tarin damammaki na cin gajiya daga babbar kasuwar kasar Sin, don haka suke ta kara fadada jarin da suke zubawa a kasuwannin kasar.

Ko shakka babu, wannan tagomashi bai zo da mamaki ba, duba da wasu matakai masu ma’ana da mahukuntan Sin suke dauka domin ingiza ci gaban tattalin arzikin kasar.

  • Zhao Leji: Zuba Jari A Sin Zuba Jari Ne Don Gaba
  • CMG Ya Kaddamar Da Wasu Sabbin Shirye-Shiryen Bidiyo Masu Amfani Da Fasahar AI

Alkaluman baya bayan nan na hukumar kididdiga ta kasar Sin, sun nuna yadda cikin watanni 2 na farkon shekarar bana, tattalin arzikin kasar ya fadada, tare da samun karin inganci. Kuma shaidu na zahiri sun nuna tattalin arzikin na Sin na da ginshiki mai karfi dake daidaita shi, baya ga babbar dama ta kara bunkasarsa a nan gaba.

Cikin manyan manufofi da kasar Sin ta kaddamar masu ingiza wannan nasara, akwai managartan matakan daidaita tattalin arziki, da ingiza bude kofa, da samar da kyakkyawan yanayin kasuwa ga masu zuba jari daga waje.

Wasu alkaluma na ma’aikatar cinikayyar kasar Sin sun nuna a watanni 2 na farkon shekarar nan ta 2024, adadin sabbin kamfanoni masu jarin waje da aka yiwa rajista a kasar Sin sun kai 7,160, wanda hakan ya nuna karuwar kaso 34.9 bisa dari na irin wadannan kamfanoni a shekara guda. Bugu da kari, darajar yawan jarin waje na kai tsaye da aka yi amfani da shi a babban yankin kasar Sin ya kai kudin Sin yuan biliyan 215.09, wato kimanin dala biliyan 30.29, inda aka yi amfani da yuan biliyan 28.27 a sashen raya manyan fasahohi kere-kere.

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

Abu ne mai faranta rai ga sassa masu zuba jarin waje, ganin yadda kasar Sin ta matsa gaba daga matakin samar da ci gaba da aka saba gani, zuwa matakin bunkasa ci gaba mai inganci, wanda ke kunshe da tarin damammaki na rasa kai, da kuma cin gajiya ga sauran sassa na kasa da kasa.

A shekarar bana, rahoton ayyukan gwamnatin kasar Sin, ya gabatar da shawarar kawar da shingaye dake shafar damammakin zuba jarin waje a sassan kere-kere, da rage wasu shingayen a fannonin bayar da hidima, kamar na fasahohin sadarwa da kiwon lafiya.

Idan mun yi hangen nesa, za mu ga cewa kasar Sin na da zarafi na ci gaba da dunkulewa tare da sauran sassan duniya, ta hanyoyinta na bude kofa a matsayin koli. Ko shakka babu, a nan gaba duniya za ta kara yin hadin gwiwa da kasar Sin bisa tafarkinta na samar da ci gaba, kuma Sin din za ta ci gaba da fadada damammakinta na hadin gwiwar cimma moriyar juna, yayin da a daya hannun za ta ci gaba da zama jigon wanzar da daidaito, a fannin bunkasa ci gaban duniya baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Next Post
Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Wakilan Amurka Suka Ce Ba Dole Ne “Tarkon Thucydides” Ya Faru Ba?

Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Wakilan Amurka Suka Ce Ba Dole Ne “Tarkon Thucydides” Ya Faru Ba?

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.