• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ke Jawo Hankalin Kamfanonin Kasa Da Kasa Zuwa Sin?

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ke Jawo Hankalin Kamfanonin Kasa Da Kasa Zuwa Sin?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya bayan nan, manyan kamfanonin kasa da kasa suna kara shigowa kasar Sin domin gudanar da hada-hadar kasuwanci, da kaddamar da sabbin hajoji, da gudanar da baje koli da dai sauransu. Kamfanonin waje na da yakinin cewa, akwai tarin damammaki na cin gajiya daga babbar kasuwar kasar Sin, don haka suke ta kara fadada jarin da suke zubawa a kasuwannin kasar.

Ko shakka babu, wannan tagomashi bai zo da mamaki ba, duba da wasu matakai masu ma’ana da mahukuntan Sin suke dauka domin ingiza ci gaban tattalin arzikin kasar.

  • Zhao Leji: Zuba Jari A Sin Zuba Jari Ne Don Gaba
  • CMG Ya Kaddamar Da Wasu Sabbin Shirye-Shiryen Bidiyo Masu Amfani Da Fasahar AI

Alkaluman baya bayan nan na hukumar kididdiga ta kasar Sin, sun nuna yadda cikin watanni 2 na farkon shekarar bana, tattalin arzikin kasar ya fadada, tare da samun karin inganci. Kuma shaidu na zahiri sun nuna tattalin arzikin na Sin na da ginshiki mai karfi dake daidaita shi, baya ga babbar dama ta kara bunkasarsa a nan gaba.

Cikin manyan manufofi da kasar Sin ta kaddamar masu ingiza wannan nasara, akwai managartan matakan daidaita tattalin arziki, da ingiza bude kofa, da samar da kyakkyawan yanayin kasuwa ga masu zuba jari daga waje.

Wasu alkaluma na ma’aikatar cinikayyar kasar Sin sun nuna a watanni 2 na farkon shekarar nan ta 2024, adadin sabbin kamfanoni masu jarin waje da aka yiwa rajista a kasar Sin sun kai 7,160, wanda hakan ya nuna karuwar kaso 34.9 bisa dari na irin wadannan kamfanoni a shekara guda. Bugu da kari, darajar yawan jarin waje na kai tsaye da aka yi amfani da shi a babban yankin kasar Sin ya kai kudin Sin yuan biliyan 215.09, wato kimanin dala biliyan 30.29, inda aka yi amfani da yuan biliyan 28.27 a sashen raya manyan fasahohi kere-kere.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Abu ne mai faranta rai ga sassa masu zuba jarin waje, ganin yadda kasar Sin ta matsa gaba daga matakin samar da ci gaba da aka saba gani, zuwa matakin bunkasa ci gaba mai inganci, wanda ke kunshe da tarin damammaki na rasa kai, da kuma cin gajiya ga sauran sassa na kasa da kasa.

A shekarar bana, rahoton ayyukan gwamnatin kasar Sin, ya gabatar da shawarar kawar da shingaye dake shafar damammakin zuba jarin waje a sassan kere-kere, da rage wasu shingayen a fannonin bayar da hidima, kamar na fasahohin sadarwa da kiwon lafiya.

Idan mun yi hangen nesa, za mu ga cewa kasar Sin na da zarafi na ci gaba da dunkulewa tare da sauran sassan duniya, ta hanyoyinta na bude kofa a matsayin koli. Ko shakka babu, a nan gaba duniya za ta kara yin hadin gwiwa da kasar Sin bisa tafarkinta na samar da ci gaba, kuma Sin din za ta ci gaba da fadada damammakinta na hadin gwiwar cimma moriyar juna, yayin da a daya hannun za ta ci gaba da zama jigon wanzar da daidaito, a fannin bunkasa ci gaban duniya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Wasan Manchester City 7 Da Zasu Iya Rasa Wasan Arsenal Sakamakon Jin Rauni

Next Post

Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Wakilan Amurka Suka Ce Ba Dole Ne “Tarkon Thucydides” Ya Faru Ba?

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

15 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

16 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

18 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

21 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

22 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

23 hours ago
Next Post
Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Wakilan Amurka Suka Ce Ba Dole Ne “Tarkon Thucydides” Ya Faru Ba?

Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Wakilan Amurka Suka Ce Ba Dole Ne “Tarkon Thucydides” Ya Faru Ba?

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.