ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ke Jawo Hankalin Kamfanonin Kasa Da Kasa Zuwa Sin?

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

A baya bayan nan, manyan kamfanonin kasa da kasa suna kara shigowa kasar Sin domin gudanar da hada-hadar kasuwanci, da kaddamar da sabbin hajoji, da gudanar da baje koli da dai sauransu. Kamfanonin waje na da yakinin cewa, akwai tarin damammaki na cin gajiya daga babbar kasuwar kasar Sin, don haka suke ta kara fadada jarin da suke zubawa a kasuwannin kasar.

Ko shakka babu, wannan tagomashi bai zo da mamaki ba, duba da wasu matakai masu ma’ana da mahukuntan Sin suke dauka domin ingiza ci gaban tattalin arzikin kasar.

  • Zhao Leji: Zuba Jari A Sin Zuba Jari Ne Don Gaba
  • CMG Ya Kaddamar Da Wasu Sabbin Shirye-Shiryen Bidiyo Masu Amfani Da Fasahar AI

Alkaluman baya bayan nan na hukumar kididdiga ta kasar Sin, sun nuna yadda cikin watanni 2 na farkon shekarar bana, tattalin arzikin kasar ya fadada, tare da samun karin inganci. Kuma shaidu na zahiri sun nuna tattalin arzikin na Sin na da ginshiki mai karfi dake daidaita shi, baya ga babbar dama ta kara bunkasarsa a nan gaba.

ADVERTISEMENT

Cikin manyan manufofi da kasar Sin ta kaddamar masu ingiza wannan nasara, akwai managartan matakan daidaita tattalin arziki, da ingiza bude kofa, da samar da kyakkyawan yanayin kasuwa ga masu zuba jari daga waje.

Wasu alkaluma na ma’aikatar cinikayyar kasar Sin sun nuna a watanni 2 na farkon shekarar nan ta 2024, adadin sabbin kamfanoni masu jarin waje da aka yiwa rajista a kasar Sin sun kai 7,160, wanda hakan ya nuna karuwar kaso 34.9 bisa dari na irin wadannan kamfanoni a shekara guda. Bugu da kari, darajar yawan jarin waje na kai tsaye da aka yi amfani da shi a babban yankin kasar Sin ya kai kudin Sin yuan biliyan 215.09, wato kimanin dala biliyan 30.29, inda aka yi amfani da yuan biliyan 28.27 a sashen raya manyan fasahohi kere-kere.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Abu ne mai faranta rai ga sassa masu zuba jarin waje, ganin yadda kasar Sin ta matsa gaba daga matakin samar da ci gaba da aka saba gani, zuwa matakin bunkasa ci gaba mai inganci, wanda ke kunshe da tarin damammaki na rasa kai, da kuma cin gajiya ga sauran sassa na kasa da kasa.

A shekarar bana, rahoton ayyukan gwamnatin kasar Sin, ya gabatar da shawarar kawar da shingaye dake shafar damammakin zuba jarin waje a sassan kere-kere, da rage wasu shingayen a fannonin bayar da hidima, kamar na fasahohin sadarwa da kiwon lafiya.

Idan mun yi hangen nesa, za mu ga cewa kasar Sin na da zarafi na ci gaba da dunkulewa tare da sauran sassan duniya, ta hanyoyinta na bude kofa a matsayin koli. Ko shakka babu, a nan gaba duniya za ta kara yin hadin gwiwa da kasar Sin bisa tafarkinta na samar da ci gaba, kuma Sin din za ta ci gaba da fadada damammakinta na hadin gwiwar cimma moriyar juna, yayin da a daya hannun za ta ci gaba da zama jigon wanzar da daidaito, a fannin bunkasa ci gaban duniya baki daya.

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Wakilan Amurka Suka Ce Ba Dole Ne “Tarkon Thucydides” Ya Faru Ba?

Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Wakilan Amurka Suka Ce Ba Dole Ne “Tarkon Thucydides” Ya Faru Ba?

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.