• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ke Shirin Faruwa Tsakanin Sarkin Katsina Da Gwamnan Jihar?

by El-Zaharadeen Umar
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Me Ke Shirin Faruwa Tsakanin Sarkin Katsina Da Gwamnan Jihar?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya asabar ne aka wayi gari da ganin wata takarda da Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Raɗɗa ya aike wa da Sarkin Katsina yana neman ƙarin bayani daga Sarkin.

An dai tura wannan takarda ne zuwa ga masarauta daga ofishin sakataren gwamnatin jihar Katsina inda ake neman Sarkin Katsina Alhaji abdulmumini Kabir Usman da ya yi ƙarin bayani akan rashin hawan wasu Hakimai a Babbar Sallah.

Takardar mai neman karin bayani kan wata takarda da aka aike a ranar 7 ga watan Yuni 2024 da lamba S/SGKT/77/S 2/T tana neman Sarki da ya yi bayanin me ya sa wasu hakamai na masarautar Katsina ba su yi hawan sallah ba kamar yadda gwamnati ta bada umarni.

Sarki

Daman dai ana ta yaɗa jita-jitar cewa dangantaka ta fara tsami tstsakani Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Raɗɗa da masarautar Katsina zargin da yanzu ke neman zama gaskiya.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Domin a baya an riƙa yaɗa labarin cewa gwamnatin jihar ta tsaida dakatar da Magajin garin Katsina wanda babban ɗa ne ga Sarkin Katsina, amma dai babu wata takarda da ta nuna hakan a gwamnatance.

Wata majiya ta ce tuni Gwamnan Katsina ya shirya kirkira wasu sabbin Hakimai a karkashin masarautar.

Shin ko me yake shirin faruwa a wannan masarauta mai daɗaɗɗen tarihi, Allah shi ne masani, tambayar da mafi yawan jama’a ke yi ke nan a halin yanzu.

Yanzu dai jama’a da dama na sauraran irin amsar da masarautar za ta maida wa Gwamnatin Jihar Katsina a kan wannan batu da ya taso.

Idan za a iya tunawa a lokacin bikin hawan Sallah ƙarama, Gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya gargadin cewa daga yanzu dole ne Kowane hakaimi ya yi hawan Sallah sai dai mai lalurar tsufa ko rashin lafiya ko kuma tafiya Makka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dikko RaddaGwamnaHakimaiKatsinaMasarautaSarautaSarkin Katsina
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Inter Miami Zan Yi Ritaya – Messi

Next Post

Wakilin MDD Ya Bukaci Daukar Matakan Gaggawa Na Dawo Da Nijeriya Turbar Manufofin Ci Gaba Mai Dorewa (SDG)

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

9 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

13 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

15 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

23 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

1 day ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

2 days ago
Next Post
Wakilin MDD Ya Bukaci Daukar Matakan Gaggawa Na Dawo Da Nijeriya Turbar Manufofin Ci Gaba Mai Dorewa (SDG)

Wakilin MDD Ya Bukaci Daukar Matakan Gaggawa Na Dawo Da Nijeriya Turbar Manufofin Ci Gaba Mai Dorewa (SDG)

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Sarki

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.