• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Hana Amurka Ta Ce “A Tsagaita Bude Wuta”?

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Hana Amurka Ta Ce “A Tsagaita Bude Wuta”?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

John Kirby, babban jami’in kwamitin kula da harkokin tsaro na fadar White House ya bayyana a gun wani taron manema labarai da aka gudanar a kwanan baya cewa, a ganin Amurka, tsagaita bude wuta, ba ita ce hanyar da ta dace ta daidaita batun Palasdinu da Isra’ila ba, don haka, ba ta fatan ganin an tsagaita bude wuta nan da nan. Ya kara da cewa, Isra’ila na ci gaba da daukar matakai na yakar manyan jami’an Hamas, kuma a ganin Amurka, kungiyar Hamas ita ce kadai ke iya amfana daga tsagaita bude wuta. Sai kuma a makon da ya gabata, mista Kirby ya ce, yanzu lokaci bai yi ba na tsagaita bude wuta a zirin Gaza. 

Sama da mutane dubu 10 na Palasdinu da Isra’ila sun halaka a rikicin da ya barke a tsakaninsu a wannan karo. Amma abin takaici shi ne tun bayan barkewar rikicin, shugaban kasar Amurka da sauran manyan jami’an kasar, duk sun yi shiru game da batun tsagaita bude wuta. Daftarin kudurin da Amurka ta gabatar ga kwamitin sulhu na MDD bai yi bayani a kan batun tsagaita bude wuta ba, baya ga haka, Amurka ta jefa kuri’ar nuna rashin amincewa da kudurin da aka zartas a babban taron MDD, wanda ya yi kira da a tsagaita bude wuta a tsakanin Palasdinu da Isra’ila.

  • Bikin Al’adu Na Inganta Mu’amalar Al’adun Sin Da Najeriya
  • An Mai Da Hankali Kan Ci Gaba Mai Inganci Yayin Taron Koli Kan Harkokin Kudi Na Sin

Ke nan me ya hana Amurka ta ce “A tsagaita bude wuta”, a yayin da ake fuskantar wannan mummunan rikicin zubar da jini?

A hakika, huldar dake tsakaninta da Isra’ila na da muhimmiyar ma’ana gare ta. Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya taba bayyanawa a jawabin da ya gabatar a shekarun da suka gabata cewa, “Da a ce babu Isra’ila, to Amurka za ta kirkiro Isra’ila don kare muradunta a yankin gabas ta tsakiya.” Kasancewar Isra’ila kasa ce mai karfi ta fannin soja da leken asiri, Amurka na daukarta a matsayin babban makaminta a yankin gabas ta tsakiya, abin da ya sa Amurka ta dade tana nuna goyon baya ga Isra’ila. A sa’i daya kuma, a kan ce babu wanda zai ci nasara daga yaki, amma abin ba haka ba ne ga masana’antun samar da makamai na kasar Amurka. Kwana uku kadai bayan barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila a wannan karo, farashin hannayen jari na kamfanin Lockheed Martin ya karu da kaso 9%, a yayin da farashin ya karu da kashi 4% ga kamfanin Raytheon, wadanda ke daga cikin manyan kamfanonin samar da makamai biyar na kasar Amurka. Kamar yadda Greg Hayes, babban jami’in kamfanin Raytheon ya bayyana a yayin zantawa da ’yan jarida a kwanan baya cewa, “yaki abu ne na bakin ciki, amma yana kawo mana cinikin makamai.”

Rikici na ci gaba, a yayin da kuke karanta wannan sharhi, ya yiwu fararen hula sun mutu ko jikkata. Amma duk wadannan ba abu ne dake gaban muradunta ba, kuma “hakkin dan Adam” da ke bakinta ya zama banza a gaban muradunta. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

Labarai Masu Nasaba

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaCGTNCMG
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutun 6 A Bauchi

Next Post

Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa

Related

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

1 hour ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

2 hours ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

3 hours ago
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

4 hours ago
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
Daga Birnin Sin

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

5 hours ago
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

23 hours ago
Next Post
Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa

Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.