ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Hana Amurka Ta Ce “A Tsagaita Bude Wuta”?

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

John Kirby, babban jami’in kwamitin kula da harkokin tsaro na fadar White House ya bayyana a gun wani taron manema labarai da aka gudanar a kwanan baya cewa, a ganin Amurka, tsagaita bude wuta, ba ita ce hanyar da ta dace ta daidaita batun Palasdinu da Isra’ila ba, don haka, ba ta fatan ganin an tsagaita bude wuta nan da nan. Ya kara da cewa, Isra’ila na ci gaba da daukar matakai na yakar manyan jami’an Hamas, kuma a ganin Amurka, kungiyar Hamas ita ce kadai ke iya amfana daga tsagaita bude wuta. Sai kuma a makon da ya gabata, mista Kirby ya ce, yanzu lokaci bai yi ba na tsagaita bude wuta a zirin Gaza. 

Sama da mutane dubu 10 na Palasdinu da Isra’ila sun halaka a rikicin da ya barke a tsakaninsu a wannan karo. Amma abin takaici shi ne tun bayan barkewar rikicin, shugaban kasar Amurka da sauran manyan jami’an kasar, duk sun yi shiru game da batun tsagaita bude wuta. Daftarin kudurin da Amurka ta gabatar ga kwamitin sulhu na MDD bai yi bayani a kan batun tsagaita bude wuta ba, baya ga haka, Amurka ta jefa kuri’ar nuna rashin amincewa da kudurin da aka zartas a babban taron MDD, wanda ya yi kira da a tsagaita bude wuta a tsakanin Palasdinu da Isra’ila.

  • Bikin Al’adu Na Inganta Mu’amalar Al’adun Sin Da Najeriya
  • An Mai Da Hankali Kan Ci Gaba Mai Inganci Yayin Taron Koli Kan Harkokin Kudi Na Sin

Ke nan me ya hana Amurka ta ce “A tsagaita bude wuta”, a yayin da ake fuskantar wannan mummunan rikicin zubar da jini?

ADVERTISEMENT

A hakika, huldar dake tsakaninta da Isra’ila na da muhimmiyar ma’ana gare ta. Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya taba bayyanawa a jawabin da ya gabatar a shekarun da suka gabata cewa, “Da a ce babu Isra’ila, to Amurka za ta kirkiro Isra’ila don kare muradunta a yankin gabas ta tsakiya.” Kasancewar Isra’ila kasa ce mai karfi ta fannin soja da leken asiri, Amurka na daukarta a matsayin babban makaminta a yankin gabas ta tsakiya, abin da ya sa Amurka ta dade tana nuna goyon baya ga Isra’ila. A sa’i daya kuma, a kan ce babu wanda zai ci nasara daga yaki, amma abin ba haka ba ne ga masana’antun samar da makamai na kasar Amurka. Kwana uku kadai bayan barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila a wannan karo, farashin hannayen jari na kamfanin Lockheed Martin ya karu da kaso 9%, a yayin da farashin ya karu da kashi 4% ga kamfanin Raytheon, wadanda ke daga cikin manyan kamfanonin samar da makamai biyar na kasar Amurka. Kamar yadda Greg Hayes, babban jami’in kamfanin Raytheon ya bayyana a yayin zantawa da ’yan jarida a kwanan baya cewa, “yaki abu ne na bakin ciki, amma yana kawo mana cinikin makamai.”

Rikici na ci gaba, a yayin da kuke karanta wannan sharhi, ya yiwu fararen hula sun mutu ko jikkata. Amma duk wadannan ba abu ne dake gaban muradunta ba, kuma “hakkin dan Adam” da ke bakinta ya zama banza a gaban muradunta. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan
Daga Birnin Sin

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci
Daga Birnin Sin

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Next Post
Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa

Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.