ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Hana Amurka Ta Ce “A Tsagaita Bude Wuta”?

by CGTN Hausa
3 years ago
Amurka

John Kirby, babban jami’in kwamitin kula da harkokin tsaro na fadar White House ya bayyana a gun wani taron manema labarai da aka gudanar a kwanan baya cewa, a ganin Amurka, tsagaita bude wuta, ba ita ce hanyar da ta dace ta daidaita batun Palasdinu da Isra’ila ba, don haka, ba ta fatan ganin an tsagaita bude wuta nan da nan. Ya kara da cewa, Isra’ila na ci gaba da daukar matakai na yakar manyan jami’an Hamas, kuma a ganin Amurka, kungiyar Hamas ita ce kadai ke iya amfana daga tsagaita bude wuta. Sai kuma a makon da ya gabata, mista Kirby ya ce, yanzu lokaci bai yi ba na tsagaita bude wuta a zirin Gaza. 

Sama da mutane dubu 10 na Palasdinu da Isra’ila sun halaka a rikicin da ya barke a tsakaninsu a wannan karo. Amma abin takaici shi ne tun bayan barkewar rikicin, shugaban kasar Amurka da sauran manyan jami’an kasar, duk sun yi shiru game da batun tsagaita bude wuta. Daftarin kudurin da Amurka ta gabatar ga kwamitin sulhu na MDD bai yi bayani a kan batun tsagaita bude wuta ba, baya ga haka, Amurka ta jefa kuri’ar nuna rashin amincewa da kudurin da aka zartas a babban taron MDD, wanda ya yi kira da a tsagaita bude wuta a tsakanin Palasdinu da Isra’ila.

  • Bikin Al’adu Na Inganta Mu’amalar Al’adun Sin Da Najeriya
  • An Mai Da Hankali Kan Ci Gaba Mai Inganci Yayin Taron Koli Kan Harkokin Kudi Na Sin

Ke nan me ya hana Amurka ta ce “A tsagaita bude wuta”, a yayin da ake fuskantar wannan mummunan rikicin zubar da jini?

ADVERTISEMENT

A hakika, huldar dake tsakaninta da Isra’ila na da muhimmiyar ma’ana gare ta. Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya taba bayyanawa a jawabin da ya gabatar a shekarun da suka gabata cewa, “Da a ce babu Isra’ila, to Amurka za ta kirkiro Isra’ila don kare muradunta a yankin gabas ta tsakiya.” Kasancewar Isra’ila kasa ce mai karfi ta fannin soja da leken asiri, Amurka na daukarta a matsayin babban makaminta a yankin gabas ta tsakiya, abin da ya sa Amurka ta dade tana nuna goyon baya ga Isra’ila. A sa’i daya kuma, a kan ce babu wanda zai ci nasara daga yaki, amma abin ba haka ba ne ga masana’antun samar da makamai na kasar Amurka. Kwana uku kadai bayan barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila a wannan karo, farashin hannayen jari na kamfanin Lockheed Martin ya karu da kaso 9%, a yayin da farashin ya karu da kashi 4% ga kamfanin Raytheon, wadanda ke daga cikin manyan kamfanonin samar da makamai biyar na kasar Amurka. Kamar yadda Greg Hayes, babban jami’in kamfanin Raytheon ya bayyana a yayin zantawa da ’yan jarida a kwanan baya cewa, “yaki abu ne na bakin ciki, amma yana kawo mana cinikin makamai.”

Rikici na ci gaba, a yayin da kuke karanta wannan sharhi, ya yiwu fararen hula sun mutu ko jikkata. Amma duk wadannan ba abu ne dake gaban muradunta ba, kuma “hakkin dan Adam” da ke bakinta ya zama banza a gaban muradunta. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa

Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.