• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Amurka Ke Jin “Tsoron” Kasar Sin Har Da Na’urar Daga Kaya Da Ta Samar?

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Jama’a, me za ku ce idan kun ji an ce “na’urar daga kaya ka iya haifar da barazana ga tsaron wata kasa”? Tabbas za ku dauki zancen a matsayin abin dariya. Sai dai an ji zancen ne a bakin wani babban jami’in kula da tashar jiragen ruwa na Los Angeles ta kasar Amurka. 

A kwanakin baya, jami’in ya ce, na’urorin daga kaya da kasar Sin ta samar ka iya haifar da barazana ga tsaron kasar Amurka, don haka kuma, gwamnatin Biden na shirin zuba biliyoyin daloli wajen samar da na’urorin a cikin gida.

  • ‘Yan Sama Jannatin Sin Sun Kammala Aikin Gyara Na’ura A Wajen Kumbo A Karon Farko
  • Yadda Sin Ke Dora Muhimmanci Ga Zamanintarwa Da Ci Gaba Mai Inganci

Duk da cewa hakan abin ban dariya ne, amma ba a rasa jin irin wadannan abubuwa cikin ‘yan shekarun baya bayan nan. Daga shigowa da kayan karafa da goran ruwa da motoci, zuwa daliban da ke dalibta a kasar, har ma da tafarnuwa da gajeren shirin bidiyo, tamkar dukkansu na iya “haifar da barazana ga tsaron kasar Amurka”. Amurka ta kusan haukacewa domin “tsoron kasar Sin”.

Amma sabo da me take wannan tsoro? In mun yi nazari, za mu gano cewa, saurin bunkasuwar kasar Sin cikin shekarun baya bayan nan ya sa wasu Amurkawa, da sauran wasu kasashen yamma damuwa da rashin jin dadi. Don haka suke son kafofin yada labaransu su yi ta yayata kalamai na wai “barazana daga kasar Sin”, tare da shafa wa kasar kashin kaza, bisa ga yadda suke zarginta da dana wa kasashe masu tasowa “tarkon bashi”, ga shi har na’urar daga kaya da ta samar na iya leken asiri……A ganinsu, kome na kasar Sin barazana ce.

Sai dai hakan ya tono mana gaskiya game da yadda Amurka ke fakewa da “tsaron kasa” wajen dakile kasashen da take dauka a matsayin abokan takara. Sanin kowa ne, Amurka ta sha yin zancen “’yancin takara” da “’yancin ciniki” a yayin da take zargin wasu kasashe da rashin ’yanci a kasuwanninsu. Amma yayin da kasashe masu tasowa ke dada bunkasa, tare da cimma nasarori wajen kirkire-kirkiren fasahohi, Amurka ita kanta kuma masana’antunta na raguwa, nan da nan sai Amurka ta manta da ‘yancin ciniki da na takara, kuma ta dauki matakai iri iri na dakile abokan takararta, da ci gaban sauran kasashe. A zahiri dai, “tsaron kasa” dalili ne kawai da ta sanar na yin kariyar ciniki da babakere, a yunkurin kare cikakkiyar moriyarta.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Sai dai a zamanin da muke ciki na dunkulewar tattalin arzikin duniya, kasa da kasa sun kasance suna cude-ni-in-cude-ka, duk wata nasarar kirkire-kirkire ta kan samu ne bisa hadin gwiwar sassan duniya daban daban. Katse huldar tattalin arziki da sauran kasashen duniya ba zai yi komai ba, illa lalata karfin kasar da ta yi hakan, da ma tsananta matsalolin da take fuskanta.

Shawara ga kasar Amurka ita ce ta mai da hankali a kan gano bakin zaren warware matsalolin da take fuskanta, kuma ta kalli ci gaban sauran kasashe yadda ya kamata, tare da rungumar hadin gwiwar kasa da kasa, hakan zai kawar da damuwarta game da kasar Sin, da ma gano hanyar kara raya kanta. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Ra'ayi Riga

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Next Post
Shettima Zai Kaddamar Da Cibiyar Horaswa Da zaƙulo Hazikan Matasa A Gombe

Shettima Zai Kaddamar Da Cibiyar Horaswa Da zaƙulo Hazikan Matasa A Gombe

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.