• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Nijeriya Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci?

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Nijeriya Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A taron dandalin hadin gwiwar kasa da kasa karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da ya gudana a birnin Beijing na kasar Sin a kwanan baya, Najeriya da kasar Sin sun zurfafa hadin gwiwarsu, inda suka kulla yarjejeniyoyin gudanar da wasu ayyuka, da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 2, wadanda suka shafi zuba jari da wasu kamfanonin Sin za su yi a Najeriya, don gina masana’antun hada motoci masu amfani da wutar lantarki, da na’urorin da suke iya shawagi da ake kira “drone”, gami da batir na motoci, da dai sauransu. 

Ban da haka, wasu kamfanonin kasar Sin 10, sun bayyana niyyar zuba jari a Najeriya don raya wasu ayyukan da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 4, wadanda suka shafi kera kayayyaki masu amfani da makamashin hasken rana, da kera motoci, da makamashi mai tsabta, da aikin gina yankin masana’antu, da na’urorin sarrafa iskar gas, da aikin koyar da fasahohin sana’o’i, da na’urorin samar da wutar lantarki masu inganci, da dai makamantansu.

  • Kasar Sin Ta Bukaci Tsagaita Wuta Da Samar Da Agajin Jin Kai A Zirin Gaza
  • An Yi Bikin Kaddamar Da Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Mutane Masu Bukata Ta Musamman Ta Asiya A Hangzhou

Bisa tantance wadannan ayyuka, za a iya ganin halayensu: Da farko, dukkansu sun shafi fasahohin zamani, da sabbin masana’antu masu kyakkyawar makoma. Na biyu, da yawa daga cikin ayyukan sun shafi yadda za a gina masana’antu da kayayyakin more rayuwa a Najeriya, kuma a tabbatar da mika fasahohi ga Najeriya, ta yadda ayyukan za su taimaki Najeriya wajen raya bangaren masana’antu. Na uku, a cikin ayyukan akwai hadin gwiwar da za a yi a fannonin koyar da ilimin sana’a, da kyautata fasahar samar da wutar lantarki, da raya tattalin arziki tare da kare muhalli, wadanda ke neman biyan bukatun Najeriya ta fuskar inganta zaman rayuwar jama’a. Wadannan halaye sun dace da taken taron Ziri Daya da Hanya Daya na wannan karo, na “aiwatar da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya cikin inganci”.

Wannan take asalinsa shi ne ra’ayin “samun ci gaba mai inganci” na kasar Sin, wanda ya shafi kokarin kirkiro sabbin fasahohi, da inganta harkoki, da kare muhalli, gami da horar da ma’aikata, don neman samun ci gaba mai inganci, da sabbin fasahohi, da kyawun muhalli, da jin dadin zaman rayuwa, ta yadda za ta tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da na al’umma mai dorewa.

Wannan ra’ayi ya riga ya zama wata muhimmiyar manufar kasar Sin a fannonin raya tattalin arziki, da gudanar da sauran ayyuka. Yanzu kasar Sin na neman yin amfani da shi wajen inganta hadin gwiwarta da sauran kasashe, da haifar musu da ci gaba, da zamanantarwa masu inganci.

Labarai Masu Nasaba

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Sai dai me ya sa kasar Sin ke son raba ilimi da dabaru, da fasahohi masu muhimmanci tare da sauran kasashe? Me ya sa take iya nuna cikakken sahihanci, a kokarinta na taimakawa Najeriya da sauran kasashen dake nahiyar Afirka samun ci gaba? Amsa ga wadannan tambayoyi ta shafi tsarin siyasa na kasar Sin.

Kasar Sin kasa ce mai rungumar tsarin siyasa na Gurguzu, hakan ya tabbatar da cewa, ba za ta yi kama da kasashen yammacin duniya ba, wadanda ke dogaro kan jari, da barin jarinsu ya yi tasiri yadda ya ga dama.

Manyan ‘yan kasuwa masu jari a hannunsu na kasashen yamma, suna son yin babakere a bangarorin fasahohi, da kudi, da tamburan kayayyaki, da shawo kan tsarin samar da kayayyaki, ta yadda za su samu karfin kare wani tsarin dake amfaninsu a duniya, don tabbatar da samun mafi yawan moriya. Wannan shi ne dalilin da ya sa kasashe masu tasowa gamuwa da wahalhalu yayin da suke neman raya tattalin arziki, a karkashin wani tsarin tattalin arziki na kasa da kasa da su kasashen yamma ke jagoranta.

A nata bangare, gwamnatin kasar Sin tana taka tsan-tsan game da illar da jari zai iya haddasawa ta rashin daidaito tsakanin al’ummu da kasashe, kana kasar ta yi kokarin kawar da gibin da ake samu tsakaninsu, don tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da na al’umma mai dorewa a duniyarmu.

Saboda haka, kasar Sin tana kokarin kawar da talauci, da kyautata zaman rayuwar jama’a a cikin gida, gami da neman samun daidaituwa, da hadin kai, da ci gaba tare a duniya, da gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya. Wannan shi ne dalilin da ya sa kasar Sin ke son ganin sauran kasashe, ciki har da Najeriya, sun samu ci gaba mai inganci. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaIsra'ilaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matashin Dan Kwallon Barcelona Guiu Mai Shekaru 17 Ya Jefa Kwallon Farko A Kungiyar

Next Post

Asalin Kungiyoyin Mayakan Hamas, Hizbullah Da Manufofinsu

Related

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

14 hours ago
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

15 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

16 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

17 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

18 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

2 days ago
Next Post
Asalin Kungiyoyin Mayakan Hamas, Hizbullah Da Manufofinsu

Asalin Kungiyoyin Mayakan Hamas, Hizbullah Da Manufofinsu

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.